رحماء بينهم
بسم الله الرحمن الرحيم
الحمد لله والصلاة والسلام على رسول الله وعلى آله وصحبه ومن والاه . وبعد
A ranar 29 ga watan Ramadan na wannan shekarar ne ta 1423B.H. na hadu da wani dattijo a cikin babban masallacin Makka mai alfarma, kuma sauraron karatu ne ya hada mu da shi. Wannan dattijon dai daga baya na fahimci cewa, shi ma malami ne kuma alKali a wata babbar kotun shari`a ta garin Kadif a Kasar Saudiyyah.
Saduwarmu da wannan malami ke da wuya sai na fahimci irin kishin da ya ke da shi game da yada addinin musulunci da gusar da yana daga aKidunsa. Nan take dai wannan bawan Allah ya fito da wani dan littafi Karami ya ba ni kyautarsa. A lokacin da na koma masaukina na samu natsuwa na karanta wannan littafi, sai na taras littafi ne mai matuKar amfani wanda ya tara ilmi mai yawa da hujjoji Kwarara masu kare martabar sahabban manzon Allah (S.A.W) daga abin da ake jingina ma su, na Kiyayya da gaba a tsakaninsu da Ahlul Baiti – iyalan gidan Manzon Allah (Allah Ya jiKansu baki daya). Ga shi kuma littafin ya Kunshi labarai masu dadi a kan zamantakewa da huldar da ke a tsakaninsu.
A lokacin da na sake nazari akan wannan littafin sai na gane ashe wanda ya ba ni littafin nan dai shi ne mawallafinsa. Don haka na yanke shawarar zan nemi izninsa akan fassara wannan littafi zuwa harshenmu na Hausa domin amfanin jama`armu. Alhamdu Lillahi, a kashegari na samu izni daga wurinsa. Allah Ya saka ma sa da mafi kyawon alherinsa, Ya ba mu aljanna firdausi akan wannan aiki mai amfani.
A nan zan so in sanar da mai karatu cewa, na yi sauye -sauye da dama a cikin wannan littafi amma ban canza ma sa ma`ana ba, sai na kusanto shi sosai zuwa ga dan uwana malam bahaushe, ta yadda mai karatu ba zai rinKa jin wani harshe ne ma a ke fassara ma shi ba. Saboda haka na Kara ma littafin nau`oin ado na magana irin ta Hausa don Kara nashadantar da mai karatu ta yadda ba zai Kosa ko ya gajiya daga karatun ba.
Kamar haka ne dai kuma na Kara inganta littafin ta hanyar koma ma littafan da mawallafin ya yi nazarinsu a wajen rubuta shi, sawa`un littafan Ahlus Sunna ko na Shi`ah, har ma na sanya lambar sifili da shafukan da aka nazarta – ga in da bai sanya ba - domin mai buKatar ya koma ga resu. Haka kuma ban yi rowa ba game da duk wani Karin haske ko sharhi wanda zai gamsar da mai karatu, amma kuma wannan sai na sanya shi a Kasan littafin, kuma da Karamin rubutu.
Fatar da ni keyi daga mai karatu ya yi mani tukuici da addu`a ta alheri, ni da mawallafinsa idan har littafin ya kasance mai amfani a ga reshi. Idan kuwa hakan ba ta samu ba, to, uzurinmu dai shi ne, mun so mu yi nasiha ne ga jama`ar musulmi, kuma muna fatar ba za mu rasa ladar wannan kyakkyawar niyyar ba.
Yanzu dai sai in ce, dan uwa a yi karatu lafiya.
Muhammad Mansur Ibrahim
Sakkwato
28 ga Zul Ki`dah 1423B.H.
Babu shakka cewa, Manzon Allah shi ne fiyayyen talikkai. Wannan abu ne da duniya duka ta sani, Kuma wata ni`imar Allah ce da Ya hada Musulmai akan sanin haka. A nan ba mu kulawa da maganganun wasu `yan tsiraru da su ke fifita sashen Imamai[1] ko Waliyyai akan Manzon Allah ta fuskar ilmi ko wani abu. Irin wadannan kalamai za ka iske wadanda suka yarda da masu fadarsu ma tawilanta su su ke yi ko kuma su raunana su.
Babu wanda yake shakka game da matsayin da Allah Ya ba ManzonSa na kasancewarsa ma`abocin ceto mafi girma, ga kuma tafkin da Allah Ya ba shi na Alkausar da sauran darajojinsa na duniya da lahira.
Haka kuma babu shakka cewa, wadannan albarkoki da alherori na Manzon Allah sun shafi iyalansa da makusantansa wadanda suka gaskata shi kuma suka taimake shi.
Saboda haka zamu ga darajojin iyalan gidan Manzon Allah suna da yawa, kuma sun zo a cikin AlKur`ani da Hadissai da dama, kuma sun hada da duk iyalansa na lokacinsa da kuma zuri`ar da suka haifa har ranar AlKiyama. Sa`annan kuma duk wasu nassoshi da suke bayyana falalar Sahabbai, to iyalan Manzon Allah na cikinsu.
A cikin littafinmu na farko mun yi bayanin darajjojin wadannan Sahabbai. A cikin wannan dan littafi kuwa zamu bayyana kyakkyawar alaKar da ke tsakanin Ahlul Baiti da Sahabbai. Bai kamata mu gajiya da Magana a kan abokantaka da manzon Allah da irin falalarta ba, da lizimtar da ke tsakanin wannan manzo mai albarka wanda albarkar zama da shi su ka samu martabar zama sahabbai. Darajojinsu kuma sun banbanta ne a aljanna daidai gwargwadon ayyukansu da jihadinsu tare da shugaban manzanni.
Haka ma a nan duniya sahabbai sun kasu kashi uku: Muhajirai da Ansarai da na bayansu kuma duk Allah Ya yi mu su alKawalin shiga aljanna. Kamar yadda Madaukakin Sarkin Ya fda in da Ya ce:
﴿لَا يَسْتَوِي مِنْكُمْ مَنْ أَنْفَقَ مِنْ قَبْلِ الْفَتْحِ وَقَاتَلَ أُولَئِكَ أَعْظَمُ دَرَجَةً مِنَ الَّذِينَ أَنْفَقُوا مِنْ بَعْدُ وَقَاتَلُوا وَكُلًّا وَعَدَ اللَّهُ الْحُسْنَى وَاللَّهُ بِمَا تَعْمَلُونَ خَبِيرٌ (10)﴾[سورة الحديد].
Ma'ana:
Wanda ya ciyar a gabanin cin nasara, kuma ya yi yaKi a daga cikinku, bay a zama daidai (da wanda bai yi haka ba). Wadancan ne mafifita girman daraja bisa ga wadanda suka ciyar daga baya kuma su ka yi yaKi. Kuma dukansu Allah Ya yi mu su wa'adi da (sakamako) mai kyau, kuma Allah Masani ne ga abin da ku ke aikatawa.
Suratul Hadid, Aya ta 10.
Haka ne. Dukkansu su na da falalarsu da darajarsu. Kuma tilas ne a kanmu mu gane girma sahibantar manzon Allah (S.A.W), mu gane cewa, wani matsayi ce mai zaman kansa. Sahabbai magabata wadanda su ka fara rungumar musulunci su na da daraja mafi daukaka. Wadanda kuma Allah Ya hada ma su biyu: tsakanin sahibtaka da zumunta – Ahlul Baiti kenan- su na da darja biyu kenan. Kuma darajojinsu na daidai da aikin ko wanensu. Allah Ya yi tsira ga resu da yarda baki daya.
Ya kai dan uwana mai karatu!
Yana da kyau ka sani cewa, tare da abin da Allah Ya Kaddara a tsakanin wadannan zababbun mutane – wadanda suka abokanci fiyayyen talikkai – na fitina da sabani wanda har ya kai zuwa ga yaKar junansu, bai hana su Kauna da rahama ga junansu ba. Wannan kuwa yana nuni zuwa ga cewa da yawan ruwayoyi da Kissoshin da ake yadawa a kansu ba gaskiya ba ne, duk kuwa da ya ke wasu marasa hankula da nazari da kuma wasu masu ra`ayoya na son zuciya sun yi anfani da wadannan ruwayoyi domin cim ma
gurinsu na fadada sabani da rikice-rikice a cikin wannan al`umma.
Zuwa ga wadanda su ka damu da yin bincike da rubutu a kan tarihin wannan al'umma, da masu kira zuwa ga hadin kan musulmi.
Zuwa ga masu Magana a kan ci gaban wannan zamani da hadarin da al'ummar musulmi ta ke fuskanta wanda ya wajabta mu hada kanmu don tunkarar matsalolinmu.
Zuwa ga duk wani mai kishin ci gaban wannan al'umma ni ke cewa, me ya sa mu ke tsokano matsaloli na tarihin al'umma da ya gabata alhalin kuwa yin haka ya na iya haifar da gaba da Kiyayya a tsakaninmu ? Me ya sa mu ke yin haka ba tare da yin nazari da bincike ba ? Don me ne ne ? Don neman jama'a ? Ko don kwaikwayon wasu ? Ko don neman wani abin duniya ?.
Sai ka tarar da wasu marubuta da masu bincike suna kashe lokaci mai yawan gaske wajen tsokaci game da wasu mas`aloli na tarihi wadanda aka gina su akan ruwayoyi masu rauni, ko aka rubuta su bisa ga son zuciya. A daidai lokacin da suke ganin sun yi KoKari akan wannan bincike in da za ka tambaye su me ne ne fa`idar abin da suka gano kuma da me ne ne zai Karashi wannan al`umma ? ba zaka samu wata amsa ba face dai wannan bincike nasu zai Kara fadada baraka da rarraba da jin takaicin juna a cikin wannan al`umma. To, a bisa wane harsashe na ilmi su ka yi wannan bincike ?.
Mun fada a littafin da ya gabata akan sahabbai cewa, aikin Manzon Allah ne wanda Allah Ya dora masa ya yi tarbiyyar wadanda Allah Ya girmama su da samun musulunta a hannunsa da abokantakarsa – wato Sahabbai – kamar yadda Allah buwayayyen Sarki Yake cewa:
﴿هُوَ الَّذِي بَعَثَ فِي الْأُمِّيِّينَ رَسُولًا مِنْهُمْ يَتْلُو عَلَيْهِمْ آَيَاتِهِ وَيُزَكِّيهِمْ وَيُعَلِّمُهُمُ الْكِتَابَ وَالْحِكْمَةَ وَإِنْ كَانُوا مِنْ قَبْلُ لَفِي ضَلَالٍ مُبِينٍ (2)﴾[سورة الجمعة].
Ma`ana:
(Allah) Shi ne Wanda Ya aika a cikin jahilai wani Manzo daga gare su, yana karanta ayoyinSa a kansu, kuma yana tsarkake su, kuma yana sanar da su littafin (AlKur`ani) da hikima (Sunna), ko da yake sun kasance daga gabaninsa lalle suna a cikin bata bayyananne.
Suratul Jum`ah, Aya ta 2.
Wadannan su ne wadanda manzon rahama da shiriya ya tsayu a kan tarbiyyarsu da karantar da su. Mun yi magana a kan lizimtar da ke tsakanin jagora (shi ne annabi (S.A.W) da rundunarsa). Manzon Allah shi ne abin koyinsu, kuma shi ne maKwaucin da su ka yi rayuwa da maKwautaka tare da shi. Manzon Allah (S.A.W) shi ne shugaban da suka kasance KarKashinsa. Su ne talakawansa, kuma su ne sahabbansa. Wannan bayanin ya gabata a littafi na farko.[2]
Ya dan uwa mai karatu!
Babu shakka a wurinka cewa manzon nan (S.A.W) ya yi kyakkyawar tsayuwa a kana bin da Allah Madaukakin Sarki Ya umurce shi na isar da manzanci da tarbiyyar sabbai da karantar da su da sauransu. Kuma sakamakon wannan tarbiyya ce su ka sami kyawawan dabi'un da a ka sansu da su, kai har ma Allah Ya kira su
﴿خير أمة أخرجت للناس﴾
Ma'ana:
"mafi alherin al'ummar da a ka fitar saboda mutane". Suratu Ali Imran, Aya ta 110.
Lura da cewa :"a ka fitar". Wa ya fitar ? Wa ya ba su wannan matsayi ?. Wannan ayar dai dai ta ke da wata ayar in da Allah Ya ke cewa:
﴿وَكَذَلِكَ جَعَلْنَاكُمْ أُمَّةً وَسَطًا لِتَكُونُوا شُهَدَاءَ عَلَى النَّاسِ وَيَكُونَ الرَّسُولُ عَلَيْكُمْ شَهِيدًا﴾[سورة البقرة ، 143].
Ma'ana:
Kuma kamar haka ne Mu ka sanyan ku al'umma matsakaiciya domin ku kasance masu bayar da shaida a kan mutane. Kuma Manzo ya kasance mai shaida a kanku.
Suratul BaKara, Aya ta 143.
Ayoyin da Allah Ya saukar a kan yabonsu su na da tarin yawa. Ga kuma wasu sun gabata ba sai mun maimaita ba.
Wannan littafi:
A cikin wannan dan littafi zan yi magana akan siffa daya ce kacal daga cikin siffofin da AlKur`ani ya bayyana Sahabban Manzon Allah da su. Wannan siffar kuwa ita ce Rahama wato tausai a tsakaninsu. Zan taKaita magana akan wannan siffa saboda dalillai kamar haka:
1- Saboda muhimmancin wannan siffa da girman ma`anonin da ta tara, kasancewarta daya daga cikin siffofin Allah da siffofin ManzonSa.
2- Allah (S.W.T) ne da kanSa Ya zabi wannan siffa a wajen yabo ga wadannan bayi naSa, Yana mai kore zace – zace da Karyace-Karyacen maruwaita. Ka duba yadda Allah Ya sifaita su da wannan siffa a cikin Suratu Muhammad in da buwayayyen Sarkin Ya ke cewa:
﴿مُحَمَّدٌ رَسُولُ اللَّهِ وَالَّذِينَ مَعَهُ أَشِدَّاءُ عَلَى الْكُفَّارِ رُحَـمَاءُ بَيْنَهُمْ تَرَاهُمْ رُكَّعًا سُجَّدًا يَبْتَغُونَ فَضْلًا مِنَ اللَّهِ وَرِضْوَانًا سِيمَاهُمْ فِي وُجُوهِهِمْ مِنْ أَثَرِ السُّجُودِ..﴾[سورة الفتح ، 29].
Ma`ana:
Muhammadu manzon Allah ne. Kuma wadannan da ke tare da shi masu tsanani ne a kan kafirai, masu rahama ne a tsakaninsu, ka na ganinsu suna masu ruku'i masu sujada, suna neman falala daga Ubangijinsu, da yardarSa. Alamarsu tana a cikin fuskokinsu, daga kufan sujuda.
Suratul Fathi, Aya ta 29.
3- Dalili na uku kuwa – ya kai dan uwana mai karatu – shi ne, la`akari da yawan gurbatattun ruwayoyi masu nuna cewa, akwai adawa da gaba a tsakanin Sahabbai har ma mutum ya kan zaci ana magana akan wasu dabbobin daji ne ba wasu mutanen kirki da Annabin rahama yayi ma su tarbiyya ba, wannan kuwa ya kan haifar da mummunar adawa da Kyama a cikin zukatan masu karatu akan magabatan nan nasu na kirki. Alhali kuwa Allah Mahalicci Ya neme mu ne da mu so wadannan bayin naSa, mu yi ma su addu`a, mu kuma nisanci Kyama da tsanuwa akansu, kamar in da Allah Ya ke cewa:
﴿وَالَّذِينَ جَاءُوا مِنْ بَعْدِهِمْ يَقُولُونَ رَبَّنَا اغْفِرْ لَنَا وَلِإِخْوَانِنَا الَّذِينَ سَبَقُونَا بِالْإِيمَانِ وَلَا تَجْعَلْ فِي قُلُوبِنَا غِلًّا لِلَّذِينَ آَمَنُوا رَبَّنَا إِنَّكَ رَءُوفٌ رَحِيمٌ (10)﴾[سورة الحشر]
Kuma wadanda suka zo daga bayansu (bayan Muhajiruna da Ansar da aka ambata a ayoyin da su ka gabata) suna cewa, `Ya Ubangijinmu ! Ka yi gafara a gare mu, kuma ga `yan `uwanmu wadanda suka riga mu yin imani, kada Ka sanya wani Kulli a cikin zukatanmu ga wadanda suka yi imani. Ya Ubangijinmu ! Lalle Kai ne Mai tausayi, Mai jinKai.
Suratul Hashri Aya ta 10.
4- Sanin dukkan wani mai bincike ne cewa, ana buKatar a tace ruwayoyi ta hanyar nazari game da maruwaitansu da kuma duba gundarin abin da suka Kunsa. To amma kuma sai ya kasance ire-iren wadannan ruwayoyi ana ta yada su ba tare da la`akari da wadanda suka ruwaito su din ba tare da kasancewar galibinsu daga cikin shahararrun maKaryata ne. Ga kuma uwa uba zamowar wadannan ruwayoyin sun zo da akasin abinda AlKur`ani kansa ya ke tabbatarwa na tsarkin zukatan wadannan bayin allah da Kaunatar juna da ke a tsakaninsu. Idan ma har ka binciki littafan da aka samo wadannan ruwayoyi a cikinsu sai ka taras irin littafan nan ne da aka wallafa su domin shaKatawa da bayar da labarurruka na ban mamaki da makamantansu, ba wai littafai ne na ilimi wadannan Malamai magadan Annabawa su ka rubuta ba.
Ya kai dan uwana mai karatu ! Ina fatar kada ka yi gaggawar yanke hukunci da yin suka da zargi don kawai abin da ya ke a cikin tunaninka na labaran tarihi, ka dakata har sai ka ji irin hujjojin da ni ke sonn in fada ma ka, domin hujjoji ne wadanda ba a saba da su ba, duk da bayyanarsu da kusancinsu da kuma Karfinsu. Haka kuma ina son in ba ka shawarar ka sake komawa a karo na biyu zuwa ga ayoyin da muka ambata ma ka a sama, ka yi ma su karatun mai basira domin ka gane maganar da ni ke fada ma ka. Musamman ma dai ka sake nazarin wadannan ayoyin guda biyu:
Aya ta farko:
﴿مُحَمَّدٌ رَسُولُ اللَّهِ وَالَّذِينَ مَعَهُ أَشِدَّاءُ عَلَى الْكُفَّارِ رُحَـمَاءُ بَيْنَهُمْ تَرَاهُمْ رُكَّعًا سُجَّدًا يَبْتَغُونَ فَضْلًا مِنَ اللَّهِ وَرِضْوَانًا سِيمَاهُمْ فِي وُجُوهِهِمْ مِنْ أَثَرِ السُّجُودِ ذَلِكَ مَثَلُهُمْ فِي التَّوْرَاةِ وَمَثَلُهُمْ فِي الْإِنْجِيلِ كَزَرْعٍ أَخْرَجَ شَطْأَهُ فَآَزَرَهُ فَاسْتَغْلَظَ فَاسْتَوَى عَلَى سُوقِهِ يُعْجِبُ الزُّرَّاعَ لِيَغِيظَ بِهِمُ الْكُفَّارَ وَعَدَ اللَّهُ الَّذِينَ آَمَنُوا وَعَمِلُوا الصَّالِحَاتِ مِنْهُمْ مَغْفِرَةً وَأَجْرًا عَظِيمًا (29)﴾ [سورة الفتح]
Ma`ana:
Muhammadu manzon Allah ne. Kuma wadannan da ke tare da shi masu tsanani ne a kan kafirai, masu rahama ne a tsakaninsu, ka na ganin suna masu ruku'i masu sujada, suna neman falala daga Ubangijinsu, da yardarSa. Alamarsu tana a cikin fuskokinsu, daga kufan sujuda.
Suratul Fathi, Aya ta 29.
Aya ta biyu:
﴿وَالَّذِينَ جَاءُوا مِنْ بَعْدِهِمْ يَقُولُونَ رَبَّنَا اغْفِرْ لَنَا وَلِإِخْوَانِنَا الَّذِينَ سَبَقُونَا بِالْإِيمَانِ وَلَا تَجْعَلْ فِي قُلُوبِنَا غِلًّا لِلَّذِينَ آَمَنُوا رَبَّنَا إِنَّكَ رَءُوفٌ رَحِيمٌ (10)﴾[سورة الحشر]
Kuma wadanda suka zo daga bayansu (bayan Muhajiruna da Ansar da aka ambata a ayoyin da su ka gabata) suna cewa, `Ya Ubangijinmu ! Ka yi gafara a gare mu, kuma ga `yan `uwanmu wadanda suka iga mu yin imani, kada Ka sanya wani Kulli a cikin zukatanmu ga wadanda suka yi imani. Ya Ubangijinmu ! Lalle Kai ne Mai tausayi, Mai jinKai.
Suratul Hashri Aya ta 10.
Karanta wadannan ayoyi, ka sake nazarinsu. Allah Ya yi ma ka jagora. Amin.
Abin da mu ka sani ne cewa, sunan mutum shi ne adireshinsa wanda ya ke nuna ko shi wane ne ko kuma wane iri ne. Da sunan mutum ka ke gane addininsa da irin hankalinsa. Misali ai ba mu taba ganin wani bayahude ya sanya sunan Muhammadu ba. Ko ka taba ganin Musulmi da sunan Lata ko Uzza?.
Saboda haka Suna yana da muhimmancin gaske. Kuma da sunan mutum ne iyayensa da danginsa da sauran jama`a su ke kiransa. Da shi ne kuma mutum ya ke banbanta da wanda ba shi ba. Don haka ne ma addinin Musulunci ya yi umurni ga uba da ya kyautata zaben suna ga `ya`yansa. Kai har ma Annabin Rahama (S.A.W) ya canza ma wasu sahabbai maza da mata sunayensu saboda rashin dacewarsu, domin iyayensu ba su zaba ma su sunaye na gari ba. Bugu da Kari babban birnin da Manzon Allah ya yi hijira zuwa ga reshi sai da ya canza ma sa suna daga Yasriba sunan da akwai ma`anar zunubi a cikinsa zuwa Daiba mai ma`anar daddadan birni.
Kamar haka ne kuma Manzo (S.A.W) ya yi nuni zuwa ga kyawawan sunaye kuma dadadansu har ma ya fadi wadanne sunaye ne mafifita a Musulunci wato Abdullahi da Abdur Rahman. Kuma ya yi nuni ga wasu sunaye da ba su dace ba kamar "Sarkin sarakuna" da makamantansu. Wannan ya sa malamai sun yawaita bincike a kan mas'alar sunaye, kuma sun wallafa littafai da dama a kan haka.
To, a nan zan yi tambaya ga reka ya kai mai karatu : Da me ka ke kiran `ya`yanka? Shin da irin sunayen da ka ke so kuma ka ke Kaunar ma`abotansu? Ko kuma da sunayen maKiyanka wadanda ka ke adawa da su kuma ka ke Kyamar su?!. Idan ka amsa wannan tambaya to, me za ka ce idan ka san cewa, Sahabban nan da ka ke jin a tarihi a na cewa, su na adawa da gaba sunayen junansu su ke sanyawa?. Ina fatar kada ka yi gaggawa har sai ka yi nazarin misalan da ni ke son kawo ma ka. Idan ka duba su sai ka yi amfani da hankalinka da basirar da Allah Ya ba ka, na tabbata za ka hango abin da na hanga a cikin yardar Allah.
Ga wasu `yan misalai a gurguje:
1- Sayyiduna Ali dan Abu Talib (R.A) yana da `ya`ya ukku wadanda ya sanya ma su sunayen Abubakar da Umar da Usman kuma dukkansu sun yi shahada a Karbala` tare da dan uwansu al- Hussain (Allah ya jiKansu baki daya).[3]
2- Al Hassan dan Ali dan Abu dalib shi ma yana da `ya`ya masu sunaye kamar haka: Abubakar da Umar da Talha su ma kuma suna daga cikin wadanda sha`anin Karbala` ya rutsa da su (Allah Ya jiKansu).
3- Al Hussaini dan Ali dan Abu dalib (wanda aka kashe a bisa zalunci da Keta a Karbala`) shi ma yana da da mai sunan Sayyiduna Umar.
4- Ali dan Hussaini dan Ali dan Abu dalib (Wanda aka fi sani Zainul Abidin) yana da `ya mace wadda ya sanya ma ta sunan A`ishah, yana kuma da da namiji mai suna Umar.
Ya kai dan uwa mai karatu ! ko akwai buKatar in ci gaba da jera irin wadannan sunaye? Ko hankalinka zai yarda cewa, wadannan bayin Allah suna adawa da junansu ne amma kuma su ka sanya ma `ya`yansu sunayen abokan adawarsu domin wata manufa ta siyasa ko wani abu?. Ka ci gaba da bincike kuma a cikin tarihin zuri`oin Ahlul Baiti kamar gidan Abbas dan Abdul Muddalib da zuri`ar Ja`afar dan Abu dalib kuma Kanen Sayyiduna Ali da zuri`ar Muslim dan AKilu dan Abu dalib da sauran Ahlul Baiti za ka yi mamakin gaske idan har kana cikin masu zaton akwai adawa a tsakaninsu da sauran Sahabbai musamman ma Khalifofin Manzon Allah guda ukku na farko(Allah Ya yarda da su).
To, daga cikin shi`awa akwai wadanda suka musanta wannan magana cewa, Sayyiduna Ali da `ya`yansa sun sanya sunayen manyan khalifofin Manzon Allah (S.A.W) guda ukku da Nana A`ishah diyar SiddiKu da makamantansu daga cikin makusantan Manzon Allah (S.A.W) domin wannan ya ci karo da abin da su ka ba da gaskiya gare shi na haifuwar adawa da gaba a tsakaninsu. Sai dai kuma malaman Shi`a kansu sun mayar da martani akan wannan magana kasancewarta a rubuce a cikin manyan littafansu, al`amarin da wasu daga cikinsu ke ganin dasisa ce ta Ahlus Sunna. Idan ko su ka bude ma kansu wannan Kofa to, mu kuma za mu tuhumce su da rashin aminta da littafansu wadanda suka bayyana sunayen nan da mu ka ambata musamman ma dai wadanda suka yi shahada a Karbala` kamar Abubakar dan Ali dan Abu dalib da Abubakar dan Hassan dan Ali. Wasu ruwayoyin ma sun bayyana Umar dan Ali da Umar dan Hassan a matsayin manyan barade wadanda suka nuna zarunta mai yawa a filin daga ranar Karbala`. To, da yaya Ahlus Sunna su ka miKa hannuwansu a cikin wadannan littafai naku su ka soka wadannan bayanai? Ashe kenan ku ma ba ku aminta ba da littafanku. Don haka sai ku bar su domin ku koma ga gaskiya. Allah Ya sa mu dace.
To, daga cikin malaman Shi`a wadanda suka nuna amincewa da gaskiyar wadannan ruwayoyi akwai masu ra`ayin cewa, Sayyiduna Ali ya sanya wa `ya`yansa wadannan sunaye ne domin taKiyyah ma`ana wai yana son ya nuna wa wadannan khalifofi cewa yana tare da su alhali a haKiKanin gaskiya shi maKiyinsu ne. Wannan maganar kuwa ita kanta suka ce babba ga matsayin Sayyiduna Ali da irin jaruntakar da aka san shi da ita, ace jin tsoronsa da rauninsa sun sanya shi har yana daukar matakai na kada aga laifinsa!. Wannan suka ce babba wadda muke nisantar da darajar Sayyiduna Ali daga irinta.
Duba wadannan sunayen da ma wasu ba su ba a cikin littafan Shi`a din kan su kamar:
1- Kashful Gummah (2/334)
2- Al fusulul Muhimmah shafi na 283
3- A`lamul Wara na Tabarsi shafi na 203
4- Al Irshad na Mufid shafi na 186
5- Al Tarikh na Ya`Kubi shafi (2/213) da sauran su.
Sakamakon Bincike:
Wannan al`amari ya tabbata haka shi ke, shahararrun magabata daga cikin Ahlul Baiti su na farin cikin sanya ma `ya`yansu sunayen Abubakar da Umar da A`ishah da Talha da makamantansu domin Kaunatayyar da ke tsakaninsu da sanin matsayinsu da darajarsu wadanda su ka ribata a sakamakon kusancinsu da Manzon Allah (amincin Allah ya tabbata gare shi). Gaskatar wannan magana kuwa yana nan a cikin AlKur`ani a cikin ayoyin da suka gabata da kuma Karshen Suratu Muhammad in da Ya ke cewa:
﴿مُحَمَّدٌ رَسُولُ اللَّهِ وَالَّذِينَ مَعَهُ أَشِدَّاءُ عَلَى الْكُفَّارِ رُحَـمَاءُ بَيْنَهُمْ تَرَاهُمْ رُكَّعًا سُجَّدًا يَبْتَغُونَ فَضْلًا مِنَ اللَّهِ وَرِضْوَانًا سِيمَاهُمْ فِي وُجُوهِهِمْ مِنْ أَثَرِ السُّجُودِ ...(29)﴾ [سورة الفتح]
Ma`ana:
Muhammadu manzon Allah ne. Kuma wadannan da ke tare da shi masu tsanani ne a kan kafirai, masu rahama ne a tsakaninsu, ka na ganin suna masu ruku'i masu sujada, suna neman falala daga Ubangijinsu, da yardarSa. Alamarsu tana a cikin fuskokinsu, daga kufan sujuda.
Suratul Fathi, Aya ta 29.
Sake karanta wannan aya ka Kara tunani a kan rahamar da Allah Ya ce akwai a tsakaninsu.
Dangantaka a tsakanin `yan adam iri biyu ce: dangantakar jini da ta auratayya. Allah Ta`ala Yana cewa:
﴿وَهُوَ الَّذِي خَلَقَ مِنَ الْمَاءِ بَشَرًا فَجَعَلَهُ نَسَبًا وَصِهْرًا وَكَانَ رَبُّكَ قَدِيرًا (54)﴾ [سورة الفرقان].
Ma`ana:
Kuma (Allah) Shi ne wandaYa halitta mutum daga ruwa, sai ya sanya shi zumunci da sarakkuta, kuma Ubangijinka Ya kasance Mai iko ne.
Suratul FurKan Aya ta 54
Sanin kowa ne cewa, aure alama ce ta yarda. Misali mutum ba zai dauki `yarsa ya bayar ga wanda ya ke shawaraki ne ba ko mutumin banza ballantana ma a ce maKiyinsa wanda ma shi ne ya kashe uwar yarinyar ko dan uwanta.
Sarakkuta tana da wani matsayi na musamman a wajen Larabawa domin kuwa ba su aurar da `ya`yansu mata sai ga wanda ya yi daidai da irin matsayin ubannensu ta fuskar dangantaka domin kada ta wulaKanta. Kishin da balarabe ya ke da shi akan `ya`yansa mata da jin sauna akan su gamu da wulaKanci shi ne ya haifar ma su da mugunyar dabi`ar nan ta turbude `ya mace da ranta da lafiyarta, al`adar da addinin Musulunci ya rosa ta, ya mayar da Larabawa bisa ga dabi`u managarta. A bisa gaskiya ma an yi ta samun yaKe-yaKe a tsakanin Larabawa wadanda musabbabinsu shi ne kishi akan `ya mace.
Haka ma a addinin Musulunci za mu samu cewa, an yi umurni da mutum ya zabi mace ta gari, haka shi ma uban diya ya nema ma ta miji na gari. Malaman FiKhu sun tsawaita bincike akan mas`alar Kafa`ah wato irin namijin da ya cancanta waliyyin mace ya amince da daura ma sa aure da ita. An yi maganganu daban-daban akan sana`ar mutum da dangantakarsa da makamantansu. Amma abin da babu sabani a kansa shi ne, wajabcin la`akari da addini ga duk wanda za`a ba shi auren mace musulma.
A game da kishi akan `ya`ya mata kuwa, Annabi (S.A.W) ya ce, duk wanda aka kashe shi a wajen kariyar irlinsa (Matarsa ko `yarsa) to, wannan mutum ya yi shahada. A dalilin keta mutuncin `ya mace guda ne Annabi (S.A.W) ya ba da sanarwar yaKi da yahudawan KainuKa`a a lokacin da wani daga cikinsu ya kware ma ta zane a kasuwa. Annabi (S.A.W) ya yi haka ne kuwa bayan ya Kulla alKawalin zaman lafiya da su, amma sai ya dauki wannan keta mutuncin `ya macce musulma da daya daga cikinsu ya yi a matsayin kwance alKawali daga bangaren yahudawan tare da abin da ya biyo bayan wannan na kashewar da wani musulmi ya yi wa wancan bayahuden dan ta'adda da kuma kashewar da shi ma yahudu su ka yi ma sa.
Haka ma idan mu ka yi la`akari da wasu hukunce-hukunce na Shari`a kamar shardanta waliyyin macce ga daura aure da wajabta shedu da haramta zina da sanya haddi ga wanda ya yi ta, duka wadannan su na nuna yadda kariyar mutuncin macce ya ke da matsayi a Musulunci.
A dalilin sarakkuta ma Shari`a ta kan haramta ma mutum auren wasu mata na har abada ko ta hana shi auren wata matuKar yana aure da wata.
Ya kai dan uwana mai karatu ! duk abin da ya gabata shinfida ce mai nuna maka cewa, auratayyar da ta gudana a tsakanin Sahabbai da Ahlul Baiti babbar alama ce ta amincewa da junansu da Kauna a tsakaninsu. Bari dai anan ma mu ba ka wasu `yan misali. Ko ka san:
1- Sayyiduna Ali dan Abu dalib ya aurar da Ummu kulsum Kanwar Hassan da Hussaini ga Khalifa Umar dan Khaddab? Ita ce kuma ta Haifa ma sa Zaidu dan Umar da RuKayyah diyar Umar. Ko kana mamakin wannan ? Me ya sa Umar ba zai auri diyar Fatima ba alhalin kuwa shi kansa baban Fatima (S.A.W) ya auri `yarsa, ita ce Hafsah Uwar muminnai ? Ko ka na ganin tsoro ne ya sa sayyiduna Ali ya aurar da 'yarsa –jikanyar manzon Allah (S.A.W)- ga surukin manzon Allah –sayyiduna Umar ? Ina jaruntakar ta sa? A wurin azzalumi ya kai ta ? Ina tsoron Allansa da kishin addininsa ? Ko ko dai ka yarda cewa, Ali ya aurar da 'yarsa ne ga Umar da ya aminta da shi da kuma addininsa ? domin ba komai a tsakaninsu ban da Karairayin 'yan shi'ah ?.[4]
2- Muhammadu dan Abubakar SiddiKu ya haifi da AlKasim wanda shi kuma ya ba da auren `yarsa Ummu farwah ga Muhammad dan Ali dan Hussain dan Ali dan Abu dalib (Wato dai jikanyar Abubakar SiddiKu ce aka hada ta aure da jikan sayyiduna Ali kuma jikan Manzon Allah (S.A.W). Ummu farwa kuwa ita ce ta haifi Ja`afar al SadiK wanda `yan Shi`ah suke dogara kacokan ga ruwayoyinsa. An ruwaito shi Ja`afar al SadiK yana cewa, Sayyiduna Abubakar ya haife ni sau biyu. Me ya sa haka? Domin daman can ita mahaifiyarsa Ummu farwa uwarta ita ce Asma`u diyar Abdul Rahman dan Abubakar SiddiK.
3- Zaidu dan Harisah – wanda shi kadai ne sunansa ya zo cikin alKur'ani- maula ne, ba baKuraishe ba. Amma saboda darajar musulunci da sahibtakar manzon Allah (S.A.W) shi ne ya auri Zainab diyar Jahsh – 'yar uwar Nana Khadijah (R.A) – wadda bayan sun rabu da ita Allah Ya daura ma manzonSa aure da ita kamar yadda ya zo a cikin suratul ahzab.
4- Usamah dan zaidu dan Harisah – wanda babansa ya gabata- manzon Allah ne ya aurar da Fatima diyar Kais – BaKuraisha – a ga reshi.
5- Salim – maulan abu Huzaifa – abu Huzaifa ya aurar ma sa da diyar dan uwansa, ita ce, Hindu diyar al Walid dan Utbah. Gidansu kuwa ya na cikin mafi girman gidajen Kuraishawa.
Auratayya a tsakanin dangin manzon Allah (Kuraishawa) da zuri'arsa a daya bangaren da kuma sauran sahabbai a bangare na biyu ta na da yawa Kwarai da gaske. Wadannan misalai ne kawai.[5]
A game da aurar da Ummu kulsum `yar Sayyiduna Ali zuwa ga Khalifa Umar kuwa wasu daga Malaman Shi`a kamar al Mufid sun ce, wai da Karfi ne Sayyiduna Umar ya dauke ta daga gidansu. Haka dai shi ma Kulini ya fada a cikin Furu`ul Kafi (6/115) A yayin da al Majlisi a cikin Mir'atul UKul (2/45) ya ke ganin wannan kuskure ne. Abin da dai ya faru ga cewarsa, shi ne, Sayyiduna Ali ya bayar da aurenta ne akan tilas bisa ga taKiyyah wato saboda jin tsoro ke nan !!. To, amma kuma Safiyyuddin al TaKtaKi ya tabbatar da wannan aure a cikin littafinsa wanda ya saw a sunan al Tusi (shafi na 58). Shi ma al Raja'i ya cirato daga Abul Hassan al Umar (Jikan Umar dan Ali dan Husaini) wanda ya ce Abbas ne dan Abdul Muttalib ya bayar da ita aure ga Sayyiduna Umar bisa ga yarda da amincewar babanta. Amma kuma shi ne ya ruwaito cewa, wai wata aljana ce ta ke fitowa da kamannun ita Ummu Kulsum a duk lokacin da mijin na ta zai sadu da ita. Ta haka ne har ta Haifa ma sa da Zaidu!!!.
Har wayau dai game da wannan aure, wani Malamin Shi`ah a wannan zamani ya ba da amsa da cewa, auren dai dai ya ke da auren Manzon Allah (S.A.W) ga Ummu Habiba diyar Abu Sufyan alhalin yana mushriki..[6]
Tabbas dai Sahabbai sun kasance suna sarakkuta da junansu ba tare da wani fargaba ba. Haka kuma su kansu Ahlul Baiti sun kasance suna bayar da auren `ya`yansu ga sauran Sahabbai. Babu shakka kuma duk mai hankali ya san wannan abu ne mai nuna aminci da Rahama da Kauna. Duk tawilolan da Malaman Shi`ah su ka yi babu wanda ya ke da wata makama ta hankali wadda ake dogara ga re ta. Domin aure abu ne da ba shi yiwuwa sai da Kauna da soyayya a tsakanin ma`aurata, sa`annan da fahimta da mutuntawa a tsakanin dangogansu. Abin da muka kawo na misalai kuwa kadan ne daga cikin abin da manazarta tarihi za su iya tsokaci a game da shi musamman auratayya a tsakanin dangin Banu Umayyah da na Banu Hashim za`a iya tattara littafi akanta. Allah Ya sa mu dace. Amin.
Dubi tabbacin abin da muka fada na auratayya a tsakanin Sahabbai da Ahlul Baiti a cikin littafan Sunna kamar:
1- Siyar A`lam al Nubala` na Dhahabi (6/258-260).
2- Tarikh al Islam na Dhahabi (6/46-47)
Sa`annan ka duba littafan Shi`ah kamar haka:
1- Al Gadir fil kitab wal Sunnah wal Adab na Abdul Hussain al Najfi (6/79).
2- Al Kafi na Kulini tare da sharhinsa Mir`atul UKul na Majlisi (3/305).
3- Al Anwar al Nu`maniyyah na Ni`imatullah al Jaza`iri (1/80).
Ya kai dan Uwana mai karatu ! Ko ka taba zama a wasu cikin abokan tafiya a aikin Hajji ko neman karatu ko tafiyar aiki ko fatauci ? Ya ya ka ji rayuwar baKunci tare da abokan tafiya?
Ko ka taba samun kanka a cikin wani matsatsi ko Kunci a gidan kaso ko a sarari? Ya ya ka ga rayuwa tare da abokai a cikin wahala? Ko ka lura da irin kusanci da Kaunatayyar da wannan zamantakewa ta ke haifarwa?
To, me za ka ce game da zamantakewar Sahabbai a Makka lokacin da fadar kalmar La`ilaha Illallahu ya kasance dalilin shiga wani Kunci da wahala?. Ka tuna tarayyar Sahabbai (irin su Abubakar SiddiKu da Ali dan Abu Dalib da Usman dan Affan da Zaidu dan Harisa) a mabuyarsu ta Darul ArKam a lokacin da ba zai yiwu ma a bayyana karatun lKur`ani ba. Sa`nnan ka tuna tarayyarsu a cikin wahalhalu da azaba da Mushrikai su ka rinKa gana ma su. Sai kuma hijirar da suka yi har sai biyu domin kubuta da addininsu zuwa Kasar Habasha. Ka tuna yadda su ka sami kansu a garin baKunci da kewa a lokacin da su ka je Madina suna masu barin dukiyoyi na gidaje da bisashe da Kaddarori daban daban, kai da ma iyalan wasu daga cikinsu.
Ka tuna irin zamantakewar Muhajirai da masu masaukinsu wato Ansar da abin da Allah Ya fada a game da su na zabin `yan uwansu akan kawunansu ga abin da su ke so kuma su ke da buKata zuwa ga reshi.
Ka tuna tarayyarsu a tafiye tafiyensu na Jihadi da Hajji tare da Manzon Allah (S.A.W) a lokacin da a Kafa ake tafiya da kuma kan raKuma, sa`adda ayari ya ke yin kwana goma a tsakanin Makka zuwa Madina kawai. A lokacin da ake tsoron dabbobin dawa ta yadda matafiyi ba zai yi shishishigin tafiya nesa da ayarinsa ba don gudun aukuwar hakan. Duba irin yadda su ke yi wa junansu murna da san barka a lokacin da suka rinjayi Mushrikai a yaKin Badar da Khaibar da makamantansu da lokacin da su ke jajanta ma junansu a yayin da Allah Ya jarabce su a Uhud da Hunain. Ashe duk wadannan ba abubuwa ne da ke Karfafa danKon Kauna da zumunci ba? Duba yadda Buwayayyen Sarki Ya ke cewa:
﴿وَاذْكُرُوا نِعْمَةَ اللَّهِ عَلَيْكُمْ إِذْ كُنْتُمْ أَعْدَاءً فَأَلَّفَ بَيْنَ قُلُوبِكُمْ فَأَصْبَحْتُمْ بِنِعْمَتِهِ إِخْوَانًا﴾[سورة آل عمران: 103]
Ma`ana:
Kuma Ku tuna ni`imar Allah a kanku, a lokacin da kuka kasance maKiya, sai Ya sanya soyayya a tsakanin zukatanku, saboda haka ku ka wayi gari, da ni`imarSa, `yan uwan juna.
Suratu Ali Imran Aya ta 103.
Haka shi ke. Ni`imar Allah ce a kansu da Ya fitar da su daga shirka wadda ta sanya su Kiyayya da gaba da yaKar junansu, Ya mayar da su ga tafarkin Musulunci suna Kaunar junansu da tausayin junansu.
Ya kai dan uwana mai karatu ! me zai hana ka yarda da abin da Allah Ya fada:
﴿... فَأَلَّفَ بَيْنَ قُلُوبِكُمْ فَأَصْبَحْتُمْ بِنِعْمَتِهِ إِخْوَانًا﴾
[سورة آل عمران: 103]
Ma'ana:
Sai (Allah) Ya sanya soyayya a tsakanin zukatanku, saboda haka kuka wayi gari, da ni`imarSa, `yan uwan juna.
Suratu Ali Imran Aya ta 103.
Ya kai dan uwa ! me zai hana ka kyautata zato ga wadannan bayi na Allah wadanda Ubangijinsu Ya ke mu su sheda, Ya ke tunatar da su da falalar da Ya yi a kansu, Ya na cewa, sun wayi gari su na 'yan uwa, zukatansu na hade, Kauna ta ke a tsakaninsu. Duba yadda Ya ce ma AnnabinSa a kansu:
﴿وَإِنْ يُرِيدُوا أَنْ يَخْدَعُوكَ فَإِنَّ حَسْبَكَ اللَّهُ هُوَ الَّذِي أَيَّدَكَ بِنَصْرِهِ وَبِالْمُؤْمِنِينَ (62) وَأَلَّفَ بَيْنَ قُلُوبِهِمْ لَوْ أَنْفَقْتَ مَا فِي الْأَرْضِ جَمِيعًا مَا أَلَّفْتَ بَيْنَ قُلُوبِهِمْ وَلَكِنَّ اللَّهَ أَلَّفَ بَيْنَهُمْ إِنَّهُ عَزِيزٌ حَكِيمٌ (63) يَا أَيُّهَا النَّبِيُّ حَسْبُكَ اللَّهُ وَمَنِ اتَّبَعَكَ مِنَ الْمُؤْمِنِينَ (64)﴾
Ma`ana:
Kuma idan (Mushrikai) sun yi nufin su yaudare ka, to, lalle ma`ishinka Shi ne Allah. Shi ne Wanda Ya Karfafa ka da taimakonSa, kuma (Ya Karfafa ka) da Mummunai. Kuma Ya sanya soyayya a tsakanin zukatansu. Da ka ciyar da abin da ya ke a bayan Kasa, gaba daya, da ba ka sanya soyayya a tsakanin zukatansu ba, kuma Allah Ya sanya soyayya a tsakaninsu. Lalle Shi ne Mabuwayi, Mai hikima. Ya kai annabi! Allah ya ishe ka da kuma wadanda su ka bi ka daga Muminai.
Suratul Anfal Aya ta 62-64.
Sai ka sake karanta wannan ayar ka gani wace irin falala ce Allah Ya yi akan ManzonSa ta hanyar Karfafa shi da Sahabbai, Kuma ya ya Allah Ya sanya Kauna a tsakaninsu, aikin da duk dukiyar duniyar nan idan an yi amfani da ita kwalliya ba za ta biya kudin sabulu ba. Har yanzu dai kana nan kana gaskata gurbatattun ruwayoyin Shi`ah masu nuna Sahabbai a matsayin masu adawa da gaba?! Ya Allah Ka ba mu basira.
Bari kuma in ba ka wani labari wanda ya fito daga daya daga cikin littafan da su ne madogarar shi`ah, ina nufin littafin Kashful Gumma na Arbulli wanda aka buga shi a Iran (2/78):
An karbo labari daga Imam Ali dan Hussaini (Zainul Abidin) yace, wasu mutane sun zo daga IraKi wurin Imam (yana nufin Ja`afar al SadiK) sai suka rinKa aukawa a cikin mutuncin Abubakar da Umar da Usman (R.A). To, a lokacin da suka Kare kalamansu sai Imam yace da su: Ku ba ni labari su wane ne ku? Shin ku ne Muhajirai na farko da Allah Ya ce:
﴿ لِلْفُقَرَاءِ الْمُهَاجِرِينَ الَّذِينَ أُخْرِجُوا مِنْ دِيارِهِمْ وَأَمْوَالِهِمْ يَبْتَغُونَ فَضْلًا مِنَ اللَّهِ وَرِضْوَانًا وَيَنْصُرُونَ اللَّهَ وَرَسُولَهُ أُولَئِكَ هُمُ الصَّادِقُونَ (8)﴾
Ma'ana:
(Ku yi mamaki) ga matalauta masu hijira wadanda aka fitar daga gidajensu da dukiyoyinsu, suna neman falala daga Allah da kuma yarda, kuma suna taimakon Allah da manzonSa! Wadannan su ne masu gaskiya.
Suratul Hashri, Aya ta 8.
Sai su ka ce, A`a. Ya ce: to, ku ne:
﴿وَالَّذِينَ تَبَوَّءُوا الدَّارَ وَالْإِيمَانَ مِنْ قَبْلِهِمْ يُحِبُّونَ مَنْ هَاجَرَ إِلَيْهِمْ وَلَا يَجِدُونَ فِي صُدُورِهِمْ حَاجَةً مِمَّا أُوتُوا وَيُؤْثِرُونَ عَلَى أَنْفُسِهِمْ وَلَوْ كَانَ بِهِمْ خَصَاصَةٌ وَمَنْ يُوقَ شُحَّ نَفْسِهِ فَأُولَئِكَ هُمُ الْمُفْلِحُونَ (9)﴾
Ma'ana:
Da wadanda suka zaunar da gidajensu (ga musulunci) kuma (suka zabi) imani, a gabanin zuwansu, suna son wanda ya yi hijira zuwa gare su, kuma ba su tunanin wata buKata a cikin Kirazansu daga abin da aka bai wa muhajirai, kuma suna fifita wadansu a kan kawunansu, kuma ko da suna da wata larura. Kuma wanda aka kiyaye shi daga rowar ransa to, wadannan su ne marabauta.
Suratul Hashri, Aya ta 9.
Sai su ka ce, A`a. Ya ce: To, ga shi ku kun sheda ba ku cikin wadannan biyun. Ni kuma na shaida ba ku cikin na ukkun su ne:
﴿وَالَّذِينَ جَاءُوا مِنْ بَعْدِهِمْ يَقُولُونَ رَبَّنَا اغْفِرْ لَنَا وَلِإِخْوَانِنَا الَّذِينَ سَبَقُونَا بِالْإِيمَانِ وَلَا تَجْعَلْ فِي قُلُوبِنَا غِلًّا لِلَّذِينَ آَمَنُوا رَبَّنَا إِنَّكَ رَءُوفٌ رَحِيمٌ (10)﴾
Ma'ana:
Kuma wadanda suka zo bayansu, suna cewa, "Ya Ubangijinmu! Ka yi gafara a gare mu, kuma ga 'yan uwanmu, wadanda suka riga mu yin imani, kada Ka sanya wani Kulli a cikin zukatanmu ga wadanda suka yi imani. Ya Ubangijinmu! Lalle Kai ne Mai tausayi, Mai jinKai.
Suratul Hashri, Aya ta 10.
Sa`annan ya ce da su: Ku fita ku bani wuri. Allah Yayi mu ku kaza da kaza (ma`ana yayi addu`a maras kyau akansu).
Ko da yake na sani duk irin wadannan ruwayoyi da su ka zo daga Ahlul Baiti `yan shi'ah su kan dauke su a matsayin taKiyya, amma mai hankali yana iya gane cewa, wannan bawan Allah gaskiya ce ya fada, don haka ba dalilin tuhumarsa da munafucci akan ya fadi gaskiya. Allah Ya sa mu dace.
Ga abin da shi kansa sayyiduna Ali ya ke cewa akan sahabbai:
Lalle, naga sahabban Annabi Muhammadu (S.A.W) kuma ban taba ganin wanda ya yi kama da su ba daga cikinku, domin su idan ka gan su da safe sai ka raina kamarsu alhalin kuwa sun kwana su na sallah. Su na da alamomi a goshinsu da kumatunsu (Alamun sallah da kukan tsoron Allah). Idan dayansu ya tuna alKiyama sai ka gan shi kamar wanda ya taka garwashi (yana zufa). Idan kuma a ka ambaci Allah sai hawaye ya dararo ma dayansu har ya jiKe rigarsa, ya rinKa girgiza irin girgizar ganye idan iska ya kada duk saboda tsoron azaba da Kaunar lada.
Fassarar Ahlul Baiti ita ce iyalan gida. Iyalan ko wane gida kuwa su ne wadanda ke cikinsa. Matar mutum ta na cikin iyalansa, haka ma `ya`yan cikinsa da ya Haifa. Malam Shari`a su kan ce Ahlul Baiti ne ga Iyalan gidan manzon Allah (S.AW) . To, amma har wa yau malamai sun yi zantuttuka mabanbantan juna dangane da su wane ne iyalan gidansa?.
Kafin mu je zuwa ga maganganun malaman sunna –ma`abuta gaskiya- ya dace mu yi nuni zuwa ga cewa, malaman shi`ah sun taKaita iyalan Annabi kawai akan `yarsa Nana Fatima da mai gidanta Ali da `ya`yansu Hassan da Husaini, sai kuma cikon imamai goma sha biyu daga cikin zuri'ar Ali.[8] Akwai kuma sabani mai yawan gaske a tsakaninsu game da wannan mas`ala. Ka duba littafin FiraKul Shi`ah na Nubakhti.
To, ga ra`ayoyan Ahlus sunna akan wadanda sunan Ahlul Baiti ya Kunsa :
Ra`ayi na daya:
Su ne wadanda Annabi (S.A.W) ya hana su cin sadaka daga cikin danginsa. Wadannan sun hada da duk zuri`ar Banu Hashim da Banul Muddalib.
Ra`ayi na biyu:
Su ne `ya`yansa da matansa da kuma zuri`arsa. Wannan shi ne zancen da Malam Ibnul Arabi ya zaba, kuma ya kafa hujjoji a kansa.
Ra`ayi na uku:
Su ne dukkan mabiyansa tun daga sahabbai har zuwa ranar tashin alKiyama. Wannan shi ne zancen da Malam Nawawi ya Karfafa. Haka ma mawallafin littafin al Insaf. Wasu kuma da su ka zabi wannan zance cewa su ka yi ana nufin da Ahlul Baiti ma su taKawa daga cikin muminai. Amma zance mafi rinjaye (ta wajen hujja) shi ne zance na farko.
Idan ka dauki ko wane littafi daga cikin littafan Ahlul Sunna wadanda su ke koyar da aKida, to, za ka tarar akwai wannan mas`ala a ciki saboda muhimmancinta.
Ba zan tsawaita ma mai karatu bayani ba, amma zan taKaita ne a kan maganar shaihun malamin nan (Ahmad dan Abdul Halim wanda a ka fi sani da) Ibnu taimiyyah.[9]
Ga maganar ta sa kamar haka:
Iyalan gidan manzon Allah (S.A.W) su na da matsayi mai girma wanda ya wajabta ma su haKKoKa a kan musulmi kamar haka:
﴿قُلْ لَا أَسْأَلُكُمْ عَلَيْهِ أَجْرًا إِلَّا الْمَوَدَّةَ فِي الْقُرْبَى﴾ [الشورى:23]
Ma`ana:
Ka ce ba ni roKonku wata lada a kansa (kiran da ni ke yi mu ku) sai dai Kauna a dangina.
Suratul Shura, aya ta 23.
Wannan shi ne ma`anar hadisin da ya gabata wanda ya ce, "Ba za su yi imani ba har sai sun so ku domin Allah da kuma kusancina". Domin manzon Allah ya hada zumunta da dukkan rassan Kuraishawa. Kuma a nan a na nufin soyayya da jibinta sama da wadda ta tabbata ga sauran musulmi.
﴿إِنَّ اللَّهَ وَمَلَائِكَتَهُ يُصَلُّونَ عَلَى النَّبِيِّ يَا أَيُّهَا الَّذِينَ آَمَنُوا صَلُّوا عَلَيْهِ وَسَلِّمُوا تَسْلِيمًا (56)﴾
Ma`ana:
Lalle Allah da mala`ikunSa Su na salati ga annabi. Ya ku wadanda su ka yi imani ! ku yi salati a gare shi, kuma ku yi sallama domin amintarwa a gare shi.
Suratul Ahzab, Aya ta 56
Dalilin shigar Ahlul Baiti a cikin wannan salati kuwa shi ne hadisin da Muslim ya ruwaito a cikin ingantaccen littafinsa daga Abu Mas`ud al-Ansari (Allah Ya Kara ma sa yarda) wanda ya ke cewa : Manzon Allah (S.A.W) ya same ni a wurin zaman Sa`adu dan Ubadah, sai Bishru dan Sa`ad y ace ma sa : Ya manzon Allah ! Allah Ya umurce mu da mu yi ma ka salati, to, yaya za mu yi ma ka salatin? Sai annabi ya yi kawaici har sai da mu ka yi fatar bai tambaya ba. Sa`annan sai manzon Allah (S.A.W) y ace : "Ku ce : Ya Allah ! Ka yi tsira ga Muhammadu da iyalan Muhammadu kamar yadda ka yi tsira ga Ibrahim da iyalan Ibrahim. Kuma ka yi albarka ga Muhammadu da iyalan Muhammadu kamar yadda ka yi albarka ga Ibrahim da iyalan Ibrahim a cikin talikkai. Lalle Kai mai godiya ne, Mai girma". Ya ce : Sannan ku yi sallama kamar yadda ku ka sani.
(Sahihu Muslim, Hadisi na 405).
Daga cikin dalillan da ke bayyana wannan haKKin na Ahlul Baiti kuma akwai hadisin Abu Humaidin al Sa`idi wanda Buhari da Muslim su ka ruwaito. Hujjoji dai a kan wannan batun su na da yawa.
Malam dan Kayyimu ya ce :
Wannan haKKi ne na su ban da sauran al`umma, ba tare da sabani akan haka ba a tsakanin Malamai.
(Jala`ul Afham Fil Salati ala khairil anam )
﴿وَاعْلَمُوا أَنَّمَا غَنِمْتُمْ مِنْ شَيْءٍ فَأَنَّ لِلَّهِ خُمُسَهُ وَلِلرَّسُولِ وَلِذِي الْقُرْبَى وَالْيَتَامَى وَالْمَسَاكِينِ وَابْنِ السَّبِيلِ﴾ [سورة الأنفال:41].
Ma`ana:
Kuma ku sani, abin sani kawai, abin da ku ka samu na ganima daga wani abu, to, Allah Ya na da humusinsa kuma don manzo, kuma saboda masu zumunta da marayu da miskinai da dan hanya…
Hadissai kuma a maganar humusi su na da yawa. Kuma rabon ya kebanci danginsa ne su kadai. Kuma ya tabbata a gare su bayan rasuwar Manzon Allah (S.A.W). Wannan shi ne zancen jumhurin malammai, kuma shi ne ingantacce.
(Al Mugni 9/288)
Fa`ida:
HaKKoKan Ahlul Baiti su na da dama. Amma dai wadannan su ne mafi muhimmanci. Kuma duk wanda nasabarsa daga manzon Allah (S.A.W) ta tabbata, kuma ya kasance musulmi, to, wadannan haKKoKan sun tabbata a gare shi. Amma kuma dole ne a kula da kyawon aiki, domin nasaba ita kadai ba ta wadatarwa. Manzon Allah (S.A.W) ya kasance ya na tsoratarwa dangane da dogara a kanta. Ga kuma abin day a aikata a makka – a cikin labarin day a shahara- in da manzon Allah (S.A.W) ya tara danginsa ya ce ma su:
Ya ku jama'ar Kuraishawa ! ku sayi kawunanku daga wuta, domin ni ba ni wadatar da ku da komai daga Allah. Ya Abbas dan Abdul Muddalib ! ba ni wadatar da kai da komai daga Allah. Ya Safiyyah gwaggon manzon Allah ! ba ni wadatar da ke da komai daga Allah. Ya Fatima diyar Muhammadu (S.A.W) ki roKe ni abin da ki ke so daga dukiyata, ba ni wadatar da ke da komai daga Allah.
Buhari ne ya ruwaito shi.
Haka kuma mun san abin da ya sauka a kan Abu Lahab (duk da dangantakarsa da manzon Allah (S.A.W). Allah Ya kare mu daga wuta.
Fa'ida:
Ya na daga cikin cikon Magana a kan matsayin Ahlul Baiti a wurinmu –jama'ar Ahlul Sunna- mu yi nuni akan matsayinmu dangane da Nawasib - wadanda su ke gaba da Ali (R.A).
Asalin kalmar Nasib ta na nuni ne ga duk wanda ya ke Kin iyalan manzon Allah (S.A.W). A cikin Kamus an fassara ta da wadanda su ke daukar Kin Ali (R.A) a matsayin addini.
Ya dan uwana mai karatu!
Kalaman da malaman musulunci su ka yi a kan yabon sayyiduna Ali da 'ya'yansa a fili ta ke. AKidarmu a kansu it ace dukkansu (Ali da Hassan da Husaini) 'yan aljanna ne. Wannan a fili ya ke. Alhamdu lillah.
A nan ina son ne in yi nuni akan matsayin Ahlul Sunna dangane da masu Kin sayyiduna Ali (R.A). Wannan mas'ala ta na da muhimmanci Kwarai da gasket, domin ta na daga cikin dalillan da suka haifar da taKin saKa da rashin jituwa a tsakanin al'ummar musulmi. Akwai kuma wadanda su ke fadada wannan baraka, su na rura wutar gaba a tsakanin musulmi, su na amfani da Karya da gangan don cimma wasu manufofinsu.
Za ka ga wani daga cikinsu idan ya yi magani sai ya zargi Ahlul Sunna da Kin sayyiduna Ali (R.A) da 'ya'yansa, ya saki bakinsa ya na zuba Karya ya na maimaita Kissoshi da wasu ruwayoyi marasa tushe wadanda a ka KirKira su don yada waccan Karya ta adawar Ahlul Sunna ga sayyiduna Ali, alhalin kuwa Ahlul Sunna su ne su ka ruwaito hadissai na gaskiya a kan falalarsa da matsayin da ya ke da shi a musulunci.
Ya dan uwana mai karatu!
Kamar yadda na fada ma ka, maganganun malammai a kan Nawasib da yawa su ke. Amma a nan zan taKaita ma ka da maganar daya daga cikinsu shi ne shaihun malamin nan Ibnu taimiyyah – Allah Ya jiKansa – wanda 'yan shi'ah su ke ganin ya fi kowa adawa da su, wanda kuma shi ne ya wallafa mafi girman littafan Ahlul Sunna na raddi a kan shi'ah. Ga abin da ya ke cewa:
Zagin Ali (R.A) da la'antarsa su na daga cikin ta'addancin da ya sa a ka kira waccan (jama'ar mu'awiyah (R.A) fi'atun bagiyah kamar yadda Buhari ya ruwaito a cikin ingantaccen littafinsa daga Khalid al hazza' daga Ikrimah ya ce: "Ibnu Abbas ya aike ni tare da dansa Ali sai ya ce ma na: ku je wajen Abu Sa'id ku saurari abin da ya ke fadi. Sai mu ka je mu ka tarar ya na gyara gonarsa. Sai ya sanya mayafinsa sannan ya zo ya nab a mu labari, har ya kawo ga zancen ginin masallaci, sai ya ce: Mun kasance mu na daukar tubali daya daya, Ammar ya na daukar biyu biyu, sai manzon Allah (S.A.W) ya gan shi, sai ya rinKa shfa ma sa Kasa ya na cewa: "kaicon Ammar , al fi'atul bagiyah za su kashe shi, ya na kiransu zuwa aljanna, su kuma su na kiransa zuwa wuta." Ya ce, Ammar ya na cewa : "ina neman tsarin Allah daga fitinu".
Kuma Muslim ya ruwaito shi daga Abu Sa'id (R.A) ya na cewa: Wanda ya fi ni alheri ya ba ni labari, Abu Katadah, cewa, manzon Allah (S.A.W) ya ce ma Ammar – a lokacin da ya ke gina rami, ya na shafa kansa ya na cewa: "kaicon dan sumayyah (ya na nufin Ammar) al fi'atul bagiyah za su kashe shi.
Wannan shi ma ya na nuna sahihancin shugancin Ali (R.A) da wajabcin biyayya a gare shi, kuma mai kira zuwa ga yi ma sa biyayya ya na kira ne zuwa ga aljanna, wanda ya ke kira zuwa ga yaKarsa kuma ya na kira ne zuwa wuta ko da kuwa ya na a kan tawili ne. Wannan kuma dalili ne a kan cewa, yaKar Ali ba ta halalta. Bisa ga haka, duk wanda ya yaKe shi ko dai ya kasance a kan kuskure saboda tawili ko kuma ya zamo mai ta'addanci ba tare da tawili ba. Wannan ita ce mafi inganci daga cikin maganganu biyu na mazhabar hambaliyyah, wato yin hukunci da kuskuren duk wanda ya yaKi sayyiduna Ali. Kuma ita ce mazhabar sauran malammai wadda daga gare ta ne su ka fitar da hukuncin halalcin yaKar 'yan tawaye ma su tawili.
Majmu'ul Fatawa na Ibnu taimiyyah (4/437).
Duba kuma in da ya ke fada a bayan wannan maganar, bayan da ya bayyana maganganun Ahlul Sunna a kan Yazid, ya bayyanar da sabanin mutane a kansa, sai ya ce:
Kuma duk wanda ya kashe Husaini, ko ya taimaka a ka kashe shi, ko ya yarda da kashe shi, to la'anar Allah da mala'iku da mutane ta tabbata a kansa.
Majmu'ul Fatawa na Ibnu taimiyyah (4/487).
To, ko ya na yiwuwa bayan haka wani mai wa'azi ko mai raya cewa shi malami ne ya yi suka ga Ahlul Sunna da cewa su ne Nawasib ? To, ga maganar daya daga cikin magabata nan ka gani. Allah Ya sa mu dace.
TSAYAWA:
Ya dan uwana mai albarka!
Yana yiwuwa tambayoyi masu yawa su dame ka dangane da abin da ka karanta cikin wannan littafi idan ka yi la'akari da abin da ka sani a tarihance game da yaKoKan da su ka gudana a tsakanin sahabbai a Jamal da Siffin ga shi kuma akasarinsu su na tare da Ali (R.A) da wadanda ke tare da shi na daga iyalan gidansa. Wannan Magana kuwa tana buKatar wani littafi wanda ni ke fatar Allah Ya taimake ni in fitar da shi nan gaba domin bayyana wannan al'amari da ire-irensa.[10]
A nan zan tunatar da kaina da mai karatu game da fada Allah da Ya ke cewa:
﴿وَإِنْ طَائِفَتَانِ مِنَ الْمُؤْمِنِينَ اقْتَتَلُوا فَأَصْلِحُوا بَيْنَهُمَا فَإِنْ بَغَتْ إِحْدَاهُمَا عَلَى الْأُخْرَى فَقَاتِلُوا الَّتِي تَبْغِي حَتَّى تَفِيءَ إِلَى أَمْرِ اللَّهِ فَإِنْ فَاءَتْ فَأَصْلِحُوا بَيْنَهُمَا بِالْعَدْلِ وَأَقْسِطُوا إِنَّ اللَّهَ يُحِبُّ الْمُقْسِطِينَ (9) إِنَّمَا الْمُؤْمِنُونَ إِخْوَةٌ فَأَصْلِحُوا بَيْنَ أَخَوَيْكُمْ وَاتَّقُوا اللَّهَ لَعَلَّكُمْ تُرْحَمُونَ (10)﴾[سورة الحجرات].
Ma'ana:
Kuma idan jama'a biyu ta muminai suka yi yaKi, to, ku yi sulhu, a tsakaninsu. Sai idan dayarsu ta yi zalunci a kan gudar, to, sai ku yaKi wadda ke yin zalunci hart a koma zuwa ga umurnin Allah. To, idan ta koma, sai ku yi sulhu a tsakaninsu da adalci, kuma ku daidaita. Lalle Allah na son masu daidaitawa. Abin sani kawai muminai 'yan uwan juna ne, saboda haka ku yi sulhu tsakanin 'yan uwanku. Ku ji tsoron Allah tsammaninku za’a jiKanku.
Suratul Hujurat, Aya ta 9-10.
Sai Allah Ya tabbatar ma su da sifar imani duk da ya ke su na yaKi da junansu. Don haka wannan aya ba ta buKatar wani dogon sharhi. Dukansu muminnai ne ko sun yaKi juna.[11]
Haka kuma ina tunatar da kai maganar Allah (S.W.T) in da Ya ke cewa:
﴿فَمَنْ عُفِيَ لَهُ مِنْ أَخِيهِ شَيْءٌ فَاتِّبَاعٌ بِالْمَعْرُوفِ وَأَدَاءٌ إِلَيْهِ بِإِحْسَانٍ﴾ [البقرة:178].
Ma'ana:
To, wanda a ka yi rangwamen wani abu gare shi daga dan uwansa, to, a bi da alheri, da biya zuwa gare shi da kyautatawa.
Suratul BaKara, Aya ta 178.
Wannan kuwa a kisan ganganci ne fa. Amma duk da haka Allah (S.W.T) Ya tabbatar da 'yan uwantaka a tsakanin wanda ya yi kisan da waliyyan wanda a ka kashe. Duk tsananin laifin mai kisan kai wanda Allah Ya tsananta uKuba a kansa amma bai fitar da shi daga da'irar muminai ba. Don haka shi dan uwa ne na musulunci ga waliyyan wanda ya kashe kamar dai yadda Allah Ya ce a waccan aya: "Abin sani kawai muminai 'yan uwan juna ne".
Wannan mas'ala dai ta na buKatar wani littafi mai zaman kansa kamar yadda na fada. Allah Ya yi ma na baiwa da samun lokacin rubuta shi ba tare da dadewa ba. Amin.
NADEWA:
Godiya ta tabbata ga Allah wanda Ya yi ma na baiwa da son manzonSa. Allah Ya dada tsira ga reshi da iyalansa tsarkakakku da sahabansa zababbu.
Ya dan uwana abin Kauna!
Bayan da mu ka tattauna a kan alaKar iyalan gidan manzon Allah (Amincin Allah ya tabbata a ga reshi) da sahabbansa zababbu (Allah Ya yarda da su) to, ya kamata mu yi ta KoKari wajen addu'a mu na roKonSa Ya yi ma na dace ga biyar abin da Ya ke so kuma Ya yarda da shi, Ya kuma sanya mu cikin wadanda bayan Ya yi yabo ga sahabbai muhajirai da ansarai su kuma Ya fade su da cewa:
﴿وَالَّذِينَ جَاءُوا مِنْ بَعْدِهِمْ يَقُولُونَ رَبَّنَا اغْفِرْ لَنَا وَلِإِخْوَانِنَا الَّذِينَ سَبَقُونَا بِالْإِيمَانِ وَلَا تَجْعَلْ فِي قُلُوبِنَا غِلًّا لِلَّذِينَ آَمَنُوا رَبَّنَا إِنَّكَ رَءُوفٌ رَحِيمٌ (10)﴾
Ma'ana:
Kuma wadanda suka zo bayansu, suna cewa, "Ya Ubangijinmu! Ka yi gafara a gare mu, kuma ga 'yan uwanmu, wadanda suka riga mu yin imani, kada Ka sanya wani Kulli a cikin zukatanmu ga wadanda suka yi imani. Ya Ubangijinmu! Lalle Kai ne Mai tausayi, Mai jinKai.
Suratul Hashri, Aya ta 10.
Kuma kamar yadda zainul abidina ya fada a lokacin da wasu jama'a daga mutanen IraKi su ka zo mi shi su na zagin khalifofi Abubakar da Umar da Usman (Allah Ya yarda da su) a lokacin da suka Kare kalamansu sai Imam ya ce da su: Ku ba ni labari su wane ne ku? Shin ku ne Muhajirai na farko da Allah Ya ce:
﴿لِلْفُقَرَاءِ الْمُهَاجِرِينَ الَّذِينَ أُخْرِجُوا مِنْ دِيارِهِمْ وَأَمْوَالِهِمْ يَبْتَغُونَ فَضْلًا مِنَ اللَّهِ وَرِضْوَانًا وَيَنْصُرُونَ اللَّهَ وَرَسُولَهُ أُولَئِكَ هُمُ الصَّادِقُونَ (8)﴾[سورة الحشر].
Ma'ana:
(Ku yi mamaki) ga matalauta masu hijira wadanda aka fitar daga gidajensu da dukiyoyinsu, suna neman falala daga Allah da kuma yarda, kuma suna taimakon Allah da manzonSa! Wadannan su ne masu gaskiya.
Suratul Hashri, Aya ta 8.
Sai su ka ce, A`a. Ya ce: to, ku ne :
﴿وَالَّذِينَ تَبَوَّءُوا الدَّارَ وَالْإِيمَانَ مِنْ قَبْلِهِمْ يُحِبُّونَ مَنْ هَاجَرَ إِلَيْهِمْ وَلَا يَجِدُونَ فِي صُدُورِهِمْ حَاجَةً مِمَّا أُوتُوا وَيُؤْثِرُونَ عَلَى أَنْفُسِهِمْ وَلَوْ كَانَ بِهِمْ خَصَاصَةٌ وَمَنْ يُوقَ شُحَّ نَفْسِهِ فَأُولَئِكَ هُمُ الْمُفْلِحُونَ (9)﴾
Ma'ana:
Da wadanda suka zaunar da gidajensu (ga musulunci) kuma (suka zabi) imani, a gabanin zuwansu, suna son wanda ya yi hijira zuwa gare su, kuma ba su tunanin wata buKata a cikin Kirazansu daga abin da aka bai wa muhajirai, kuma suna fifita wadansu a kan kawunansu, kuma ko da suna da wata larura. Kuma wanda aka kiyaye shi daga rowar ransa to, wadannan su ne marabauta.
Suratul Hashri, Aya ta 9.
Sai su ka ce, A`a. Sai ya ce: To, ga shi ku kun sheda ba ku cikin wadannan biyun. Ni kuma na shaida ba ku cikin na ukkun, su ne:
﴿وَالَّذِينَ جَاءُوا مِنْ بَعْدِهِمْ يَقُولُونَ رَبَّنَا اغْفِرْ لَنَا وَلِإِخْوَانِنَا الَّذِينَ سَبَقُونَا بِالْإِيمَانِ وَلَا تَجْعَلْ فِي قُلُوبِنَا غِلًّا لِلَّذِينَ آَمَنُوا رَبَّنَا إِنَّكَ رَءُوفٌ رَحِيمٌ (10)﴾
Ma'ana:
Kuma wadanda suka zo bayansu, suna cewa, "Ya Ubangijinmu! Ka yi gafara a gare mu, kuma ga 'yan uwanmu, wadanda suka riga mu yin imani, kada Ka sanya wani Kulli a cikin zukatanmu ga wadanda suka yi imani. Ya Ubangijinmu! Lalle Kai ne Mai tausayi, Mai jinKai.
Suratul Hashri, Aya ta 10.
Sa`annan ya ce da su: Ku fita ku bani wuri. Allah Yayi mu ku kaza da kaza (ma`ana yayi addu`a maras kyau akansu).
Ya na da kyau mu sani cewa, duk yadda gaskiya ta bayyana, hujja ta tsayu, mutum ba zai wadatu daga Ubangijinsa ba (wajen shiriyarsa). Ga shi dai har Allah Ya aiko manzonSa da Kwararan hujjoji, da alKur'anin da ya ke haske ne bayyananne kamar yadda Allah Ya fada, ga kyawon dabi'un manzon Allah nagartattu tare da Karfin bayaninsa da yawan fasaharsa da kyawon halinsa, ga shi kuma mutanen makka sun san ba ya Karya ko can dadai a Kuruciyarsa, amma duk da haka dai wasu mutanen makka su ka yi zamansu a kan kafircinsu (su na ta famar fada da musuluncin) har sai da Allah Ya shigar da addininsa a ga resu ta hanyar buda garin makka. Don haka mu nace wajen roKon Allah Ya yi ma na dace, Ya tabbatar da mu a kan gaskiya da biyarta duk in da ta ke domin shiriya daga wurin Allah (Mai girma da daukaka) ta ke.
Dan uwana mai alfarma!
Ka tuna cewa, lalle ana nemanka da bin umurnin Allah, kuma Allah Zai yi ma ka hisabi a kan haka. To, ka ji saunar gabatar da maganar wani a kan ta Allah (S.W.T), ga shi Allah Ya saukar ma ka da alKur'ani da harshen larabci bayyananne, Ya sanya shi ya zamo shiriya da waraka ga muminai, ya zamo makanta ga wadanda ba su ba. Kamar yadda Allah Ya ce:
﴿قُلْ هُوَ لِلَّذِينَ آَمَنُوا هُدًى وَشِفَاءٌ وَالَّذِينَ لَا يُؤْمِنُونَ فِي آَذَانِهِمْ وَقْرٌ وَهُوَ عَلَيْهِمْ عَمًى﴾[سورة فصلت:44].
Ma'ana:
Ka ce, "Shi, shiriya ne da waraka ga wadanda suka yi imani. Wadanda ba su yi imani ba akwai wani nauyi a cikin kunnuwansu, kuma shi wata makanta ne a kansu.
Suratu Fussilat, Aya ta 44.
Saboda haka ka dage akan biyar sawun alKur'ani. Allah Ya yi ma ka dace da yardarSa.
Ya kai mai albarka!
Ka tuna cewa, hisabin talikkai gaba dayansu na Allah ne. Ba wanda zai yi wani abu a ciki, sai ceto ga mutanen kirki idan Allah Ya ba su iko. Mu daina yi wa Allah shishshigi mu na yanke hukunci a kan bayinSa.
Son iyalan gidan manzon Allah (S.A.W) da sauran sahabbansa (Allah Ya yarda da su gaba daya) ba zai cuta ma na ba, domin ma shi ne ya yi daidai da alKur'ani mai girma da ruwayoyi ingantattu. Sai ka yi nazarin wannan.
Daga Karshe, ina kiranmu da mu yawaita addu'a domin Allah Ya cire ma na ko wace irin Kyama (akan musulmi) daga cikin zukatanmu. Ya lurar da mu gaskiya, Ya taimake mu a kan kawunanmu da kuma a kan shaidan. Allah Shi ne Majibincin haka kuma Mai ikon yin hakan.
Allah Shi ne Mafi sani.
Tsira da aminci su tabbata ga annabinmu Muhammadu da iyalansa da sahabbansa.
Fassara ta kamala a yau daren Laraba 7 ga watan Rajab 1424 a tsibirin Bictoria, Lagos.
Godiya ta tabbata ga Allah Ubangijin talikkai.
[1] Al majlisi a cikin Bihar al Anwar ya Kulla babi da ya sa ma sa suna: "Babi a kan cewa, Imamai sun fi Annabawa ilmi" (2/82). Duba kuma: Usul al Kafi na Kulini (1/227). – Daga mai littafi.
[2] Sahabbai su ne almajiran Manzon Allah wadanda aka ce ya tsarkake su. Idan mun kira shi Liman, to su ne Mamunsa, Idan kuma mun ce kwamanda, to su ne sojojinsa. Idan ya kasance shugaba, har wa yau su ne talakawansa. Idan kuma an umarci Manzo da ya karbi zakka to daga wurinsu ne zai karba. Idan kuma an ce ya bayar da ita, su din ne zai bai wa. Haka ma idan an umurce shi da ya kyautata ma maKwauta, to su ne maKwautan nasa. Don haka, ba zai yiwu a raba daya biyu ba. Idan har mutun ya yi suka ga wadannan almajirai to, yana zargi ne da tuhuma ga malaminsu. Mu kam dai Ahlul Sunnah mun yi amanna cewa, Manzon Allah (S.A.W) ya yi aikin da aka dora ma sa na yi masu tarbiyya kyakkyawa wadda a sakamakonta ne suka siffaitu da kyawawan dabi`un da suka hada da Kaunar junansu da jin tausayi a tsakaninsu har suka zamo al`umma mafi alheri wadda aka fitar ma mutane. (Duba AlKur`ani, Suratu Ali Imrana, Aya ta 110). Siffofin wadannan Sahabbai kyawawa suna da tarin yawa. Kuma duk wanda yake karanta AlKur`ani ya san da haka.
[3] Al`amarin da ya faru a Karbala` yana da ban takaici a cikin tarihin wannan al`umma. Amma kuma Allah Ya riga Ya rubuta faruwarsa, ya kuma faru din a bisa ga yadda Allah Ya Kaddara shi. Wajibinmu a yanzu shi ne, mu kwatanta adalci a game da jingina laifin kisan Husaini da `yan uwansa da wasu daga cikin iyalinsa. Dalili kuwa shi ne, ruwayoyi sun sha banban da juna akan wannan lamari. Kuma babu shakka cewa, Yazidu dan Mu`awiyah bai yi umurni da a kashe su ba, bai kuma yi farin ciki akan kisan su ba. Abin da ya yi umurni da shi shi ne a hana su isa IraKi in da `yan shi`a su ka yi alKawalin nada Husaini a matsayin shugaba na biyu bayan kuwa ga tsayayyen shugaba wanda ke gudanar da mulki, wato Yazidu. To, a fagen nan fa na tare su daga isa birnin IraKi Allah Ya hukunta al`amarinSa in da wasu tsiraru su ka kai farmaki akan su bayan duk tattaunawar da aka yi ba ta ci nasara ba. Yazidu kuma ya nuna damuwa ainun akan wannan abin da ya auku, ya kuma yi rantsuwa cewar bai yi umurni da haka ba, kuma ba haka ya ke nufi ba. Amma ina abin yi bayan mai aukuwa ta riga ta auku?. Allah Ya kare mu daga fitina.
[4] Bayan rasuwar sayyiduna Umar (R.A) Abdullahi dan Ja'afar dan Abu dalib shi ne ya aure ta.
[5] Daga cikin auratayyar da ya kamata mu sani a tsakaninsu akwai auren da Sayyiduna Ali dan Abu dalib ya yi da matar Khalifa Abubakar SiddiKu a bayan rasuwarsa. Wannan matar ita ce Asma`u Bintu Umais wadda daman can matar Ja`afar ce Kanen Sayyiduna Ali kafin ya samu shahada a yaKin Mu'uta wanda manzon Allah ya tura shi. Bayan rasuwarshi sai ta auri Abubakar. Asma`u kuma ita ce ta haifi Muhammadu dan Ja`afar, sa`annan da ta auri Abubakar shi ma ta haifa ma sa Muhammadu. A wata rana wadannan `ya`yan nata sun yi jayayyar daraja a gaban mijinta Sayyiduna Ali, sai ya ce ma ta, ki raba ma su gardama mana! Ita kuma sai tace, to, kai dan Ja`afar Babanka ba irinsa a cikin matasa. Kai kuma dan Abubakar Babanka ba irinsa a cikin dattijai. A cikin raha da nashadi irin na mata da miji sai Ali ya ce ma ta, to wa ya rage kenan? Yana nufin shi a wane matsayi ta ajiye shi?.
To, a yanzu dan Uwa ko ka lura da yadda sarakkuta ta ke a tsakanin Ahlul Baiti kansu da sauran Sahabbai? Ko ka shaKi Kanshin wata adawa tana gudana a tsakaninsu? Ko ko dai ka lura al`amarin nasu yadda Allah Ya fade shi ne a ayoyin da malam ya kawo ma ka su a baya?
Ko ka na iya lura tare da ni cewa, wanda ya ke suka ga surukanka kai din ne ya ke suka a gare ka? Manzon Allah (S.A.W) da kansa ne ya auri `yar gidan Abubakar (Nana A`ishah), sa`annan ya auri `yar gidan Umar (Nana Hafsah), sa`annan ya aurar da `yarsa RuKayyah ga Usman, da Allah Ya yi ma ta cikawa sai ya sake ba shi wata `yar ta sa Ummu Kulsum, ita ma a lokacin da ta cika Annabi (S.A.W) yace ma sa, a yanzu ba ni da wata `ya da na Kara ba ka ita. To, saboda Allah idan `yan Shi`a su ka ce, wadannan mutanen, Abubakar da Umar da Usman duk ba mutanen kirki ba ne to, wa su ke nufin ba ya da kirki?!.
[6] Wannan magana abar haushi ce, abar dariya!. Domin kuwa shi Manzon Allah shi ne ya aura, ba aurar ma Abu Sufyan ya yi ba. Kuma ita Ummu Habiba musulma ce shi ya sa manzon Allah Ya aure ta. To, a ina ku ka sami musulmi ya aurar da 'yarsa ga wanda ku ka ce kafiri ne ?.
Malam bai yi magana game da matsayin malaman shi'ah ba a game da auren manzon Allah (S.A.W) da wadannan tsarkakakkun `ya`ya na Abubakar da Umar (Ina nufin Nana A`ishah da Nana Hafsah), a kan haka na ga ya dace in yi taKaitaccen sharhi a kai. To, a haKiKanin gaskiya malaman shi'ah ba su fitowa fili su yi suka ga auren wadannan mata da manzon Allah (S.A.W) yayyi, amma su kan yi suka ga su matan a cikin littafansu. Misali Ni`imatullah al Jaza`iri a cikin littafin Al Anwar al Nu`maniyyah (1/108) ya yi suka ga Nana A`ishah da cewa, wai tana adawa da Nana Fatima diyar Manzon Allah (S.A.W). Haka ma Muhammad BaKir al Majlisi a cikin littafin Mir`atul UKul (3/305) cewa ya yi ta na adawa da Allah da ManzonSa da duk Ahlul Baiti. A yayin da shi kuma Abdul Hussain al Najfi a littafinsa al Gadir (6/79) suka ya yi ga Nana Hafsah yana mai cewa, wai ba ta san wankan janaba ba ! Subhanallah ! To, wane ne bai koya ma ta ba kenan?!
[7] Wani abu mai muhimmanci da ba a cika mayar da hankali gare shi ba shi ne, ayyukan da sayyiduna Ali (R.A) ya yi a KarKashin gwamnatocin da su ka gabace shi. Sai kuma yaKoKan da ya yi tare da su kamar yaKin ridda wanda sayyiduna Abubakar ya yi a kan Banu Hanifa in da can ne sayyiduna Ali ya samu kuyangar da ta Haifa ma sa shahararrren dan nan nasa Muhammad wanda a ke ce ma sa Ibnul Hanafiyyah (a cikin bangaroran shi'ah akwai wadanda su ke sanya shi cikin Imamai goma sha biyu). Ko ka yarda cewa, duk cikin bai yarda da sahihancin mulkinsu ba ne ya yi ma su aiki, kuma ya yi yaKi tare da su har ya halaltar da samun rabo a cikin bayi ?
[8] Sauran `ya`yan manzon Allah guda shida da matayensa da har sauran zuri`ar Ali din kansa kamar Ummu kulsum diyar Fatima wadda sayyiduna Umar ya aura duk ba su samu shiga a ciki ba saboda son ran `yan shi`ah.
[9] Maganar wannan malami a nan ta na da muhimmanci Kwarai da gasket saboda dalillai guda uku:
1- Domin taKaicewarta
2- Domin gamewar ma`anarta
3- Domin malamin ya na cikin wadanda `yan shi`ah su ke ganin kamar ya fi kowa adawa da su, saboda littafinsa da ya wallafa Minhajul Sunnatin Nabawiyyah wanda ya ragargaza aKidunsu a cikinsa da hujjoji mabayyana.
[10] Wannan mas'ala a bisa gaskiya bai kamata a bar mai karatu ba tare da Karin haske a kan ta ba. Bisa ga haka ni ke cewa, sahabbai sun kasu kashi uku dangane da rikicin da ya faru a tsakanin khalifa sayyiduna Ali (R.A) da gwamnan Kasar sham sayyiduna Mu'awiyah (R.A). Jama'a ta farko su ne wadanda su ka taimaki shugaba a kan wanda su ke ganin ya yi ma sa tawaye. Wadanda suka dauki wannan matsayi su ne mutanen Kufa da na Basrah. Akwai kuma daga cikin sahabbai Abdullahi dan Abbas da Ammar dan Yasir wanda a dalilin kashe shi wadannan jama'a sun samu Kwarin gwiwa sosai saboda hadisin da shaikhul islam ya kawo na cewa azzalumai zasu kashe shi.
Jama'a ta biyu su ne wadanda su ka taimaki Mu'awiyah a kan cewa, shi ya na yaKi ne ba domin yin tawaye ga Ali ba, sai don neman jinin dan uwansa sayyiduna Usman (R.A) wanda a ka kashe shi a madina ya na khalifa, kuma suna ganin kasawar sayyiduna Ali a kan wannan al'amari mai muhimmanci. Wadannan su kuma su na hujja da aya ta 33 a cikin Suratul Isra'i wadda ta ba da dama ga waliyyi ya dauki fansar dan uwansa da a ka kashe, har ma Allah (S.W.T) Ya yi alKawalin zai taimaka ma sa. Mafi yawan mutanen Makka da na Sham suna da wannan ra'ayin wanda ya sa ba su yi ma Ali mubaya'a ba, ba domin ganin bai cancanta ba, sai dai don suna ganin ba shi ne ajandar wannan lokacin ba. Daga cikin wadanda suka dauki wannan matsayi har wayau akwai Amru dan Asi da Ka'abu dan Malik da Zubairu da Dalhatu da Nana A'ishah da Ya'ala dan Abu Umayyah.
Jama'a ta uku kuwa su ne wadanda su ka Kaurace wa al'amarin gaba daya, ba su taimaki ko wane bangare ba daga cikin masu fada da juna. Hujjar wadannan jama'a ita ce, wannan yaKi fitina ne, kuma manzon Allah (S.A.W) ya yi umurni da a aje makami a lokacin fitina. Suna hujja da hadissai da dama kamar wanda Bukhari ya ruwaito daga manzon Allah (S.A.W) cewa: "Fitina za ta kasance a nan gaba. Wanda ya yi kwance a cikinta ya fi wanda ya zauna, wanda ya zauna ya fi wanda ya tsayu, wanda ya tsayu ya fi wanda ya yi tafiya a cikinta". Wannan ra'ayi shi ne mafi rinjaye a cikin sahabbai, kuma shi ne ra'ayin Abu Mas'ud al Ansari da Sa'adu dan Abu WaKKas da Muhammadu dan Maslamh da Abdullahi dan Umar da Abu Musa (R.A) wanda Ali ya yarda ya wakilce shi a kan sulhu duk da ya ke bai yi yaKi tare da shi ba (a dalilin rashin goyon bayansa ga yaKin ne ma Ali ya cire shi daga gwamnan Kufa ya sanya Kuraza dan Ka'ab wanda ya ke goyon bayan shi Ali). Duk wanda ya ke karanta wadannan labarai da natsuwa da nazari mai kyau zai gane cewa, lallai an sami gibi na musayar bayanai wadanda su ka haifar da Karancin fahimta da munana zato daga ko wane bangare, musamman ma idan mu ka yi la'akari da manufar ko wannensu a kan yaKin. Ga kuma 'yan fitina wadanda su ne su ka kashe sayyiduna Usman su na Kara rura wuta a duk lokacin da bangarorin biyu su ka yi kusa da fahimtar juna. Za mu iya gane wannan idan mu ka duba yadda yaKin jamal ya tashi bayan an wayi gari a kan sulhuntawa, da kuma yadda kwamitin Abu Musa (R.A) da Amru dan Asi (R.A) ya kasa cim ma hanyar da za ta dakatar da yaKi nan take. Duba cikakken tarihin wannan al'amari a cikin Fathul Bari (13/53-59) da Albidayah wal Nihayah .
[11] Ya na yiwuwa mai karatu ya ce, to, ya kuma hadisin da ya ce: "Idan musulmai biyu su ka hadu da takubbansu, da wanda ya kashe da wanda a ka kashe duk su na cikin wuta.." fa ? Amsar wannan tambaya biyu ce. Da farko ayar ba ta ce kafirai ne ba, kuma ba duk wanda a ka ce zai shiga wuta kafiri ne ba. Akwai zunubbai da dama da a ka ce wanda ya yi su zai shiga wuta ba domin ya kafirta ba. Kuma ya na iya haduwa da rahamar Allah sai ya zan bai shige ta ba.
Na biyu, wannan aya ta na Magana ne a kan masu fada wanda ba na lokacin fitina ba, kamar wadanda su ke fada a kan wani al'amari na duniya. Amma yaKin da ya ke na fitina in da ko wane bangare ya ke ganin ya na da hujja, kuma ma jihadi ne ya ke yi, to, babu shakka wannan ba shi ayar ta ke nufi ba.