WASU HADISAI ARBA'IN GAME DA AL-QUR'ANI ()

WASU HADISAI ARBA'IN GAME DA AL-QUR'ANI

|

 WASU HADISAI ARBA'IN GAME DA AL-QUR'ANI

 Gabatarwar Muftin Alkali na Musamman Shehin Malamin Hadisin nan: Salih Bn Sa'ad Al-luhaidan - Allah Madaukaki ya kare shi -

Da sunan Allah Mai Rahama Mai jin kai

Godiya ta tabbata ga Allah wanda ya saukar da littafin sa Mai Hikima da kuma Shiriya Hukunci Gaskiya da kuma Tafarki Madaidaici.An Saukar da shi ga Mafificin Halittarsa da Manzanninsa - Amincin Allah a gare su - Annabi Muhammad tsira da Amincin Allah su tabbata a gare shi don ya tsaya wajen isar da shi ga baki dayan su har zuwa ranar da za'a tashe su.Bayan Wannan Hakika Dana Shiekh Ahmad Bn Abdurrazak Bn Muhammad Bn Zayid Al-angari ya gabatar mun kwafi na littafinsa HADISAI ARBA'IN GAME DA AL-QUR'ANI wanda ya kunshi Falalolin Alqur'ani Maigirma da kuma abin da ya a san shi da kuma aiki da shi ta hanyar Iklasi da gasgata aiki da kuma kubutacciyar Niyya ga barin abin da zai bata ta.Kuma babu wani laifi to duk wanda yayi duba na nutsuwa ga abinda Shiekh Ahmad ya kawo a littafinsa zai same shi cewa ana matukar bukatar kwatankwacin irin wannan a wannan lokaci wanda ya yake bukatarsa, Ya wajaba ga Musulmi ya sani kuma ya kiyaye hakikanin Hukunce hukuncen Addininsa da Duniyarsa ta hanyar Alqur'ani da Ingantacciyar Sunnakuma hakika ya zo daga Dan Umar cewa shi ya ce: bama wuce Ayoyi goma har sai mun koyi Ilimi da kuma aiki da shi daga cikin suKuma Alqurani Maigirma da Sunnanar Annabi dole ne a koye su daga Bakin Malamai wadan da suka hada tsakanin Ilimi da Hadda da kuma Fahimta da kyakkyawar fahimta ta hakikanin abin da nassi yake nufi cikin manufofin Rayuwar Duniya da lahira na abinda ya hada tsakanin Maganganu da kuma Ayyuka

kuma Rubuta wadan nan hadisan Alqurani bana zaton Shiekh Ahmad yana nufin ya gama tare baki dayansu domin wasu daban da yawa sun zo suna nan a tattare a cikin Manyan litattafan Hadisi guda Shida da wajensu Kamar Musnad na Imam Ahmad da Al-musannaf Na Abdurrazak da Musannaf na Ibn Abi Shaibah, da Sahihin ibn Hibban da Musnad na Sa'id Bn Masour da wasun su na tushen Musulunci, sai dai yana nufin fadakarwa zuwa Muhimmanci da kuma falalarsa da haddace shi da kuma kyakkyawan Nazarinsa ta hanyar wa'azantuwa da Ayoyinsa ba wai don tarawa ba da kuma haddace shi da aikata shi da Hukunci da abinda yake faruwa na Hukunce Hukuncen Sababbin abubuwa sababbi da suke faruwa.

kuma ya isa Daukaka ga Mahaddacin Qur'ani cewa shi ana bashi lada kan Haddarsa , kuma qurani zai cece shi, kuma ana samun waraka da shi kuma ana samun Albarkar samunsa da shi daidai da yadda ya kyautata niyyarsa da kuma jin Tsoransa da tsantseninsa.

To Allah Madaukaki yayi Albarka a kokarin Shiekh Ahmad Al-Ibrahim Al-Angary kuma ya amfanar da Ilimin sa kuma ya kuma Karfafe shi domin cewa shi Mai yawan kyauta ne kuma Mai baiwa

Wanda ya rubuta shi

Salih Bn Sa'ad Al'luhaidan

1428/1/17 Bayan Hijira

 Gabatarwar Shehin Malami Masanin Hadisi Abdullahi Bn Abdurrahaman Al-sa'ad - Allah ya tsare shi -

Da sunan Allah Mai Rahama Mai jin kai

Godiya ta tabbata ga Allah Ubangijin talikai kuma tsira da Aminci su tabbata ga Manzon Allah tsira da Aminci su tabbata a gare shi. Bayan haka kuma

To hakika na karanta littafin Dan mu Shiekh Ahmad Bn Abdurrazak Bn Muhammad Al-Ibrahim Al-angary Allah ya datar da shi.

wacce ta tare Hadisai Arba'in na Falaloli da Hukunce Hukunce da kuma Ladaban Alqur'ani Maigirma, kuma hakika ya kyautata wajen taro su kuma ya amfanar, to Allah ya saka masa da Alkairi.

kuma wannan Maudu'i yana daga cikin Maudu'ai Muhimmai sabo da dangantakar sa da littafin Allah Maigirma da Daukaka

Kuma daga cikin Mafi girman Ayyukan neman lada wadan da Bawa zai kusanci Ubangijinsa da su Nazarin Ayayoyinsa kamar yadda Allah yace cikin littafinsa: "Littafi ne da muka saukar da shi a gareka mai Albarka don kuyi nazarin Ayoyinsa"

Ibn Al-qayyim ya ce: a cikin Fa'idodi: littafi na 1 a shafi na 3Wata Babbar Ka'idaIdan kanason Amfani da Qur'ani to ka taro zuciyarka wajen Karatunsa da jinsa, kuma kabada jinka, ka halarto da zuciyarka da wanda kake magana da shi mai tsarki, to cewa zancensa, wanda yazo ta hanyar Manzonsa.Allah Madaukaki ya ce"Lalle ne, a cikin wancan, akwai tunãtarwa ga wanda zũciyarsa ta kasance gare shi, kõ kuwa ya jẽfa saurãro, alhãli kuwa yanã halarce (da hankalinsa).Suratu Kaaf: 37

kuma wannan cewa cikar Tasirin ya kasance yana nan ne kan Tasirin abun da ake karantawa, kuma nan Mahallin karba, kuma Sharadin samun Tasirin, kuma da kore duk wani abun da zai hana hakan, kuma Ayar ta kunshi bayanin hakan baki dayan sa da dunkulallun lafazansa da gininsa, da kuma nuninsa kan Manufarsa.

Da fadinsa: Lalle ne, a cikin wancan, akwai tunãtarwaSurat Kaaf: 37Nuni zuwa ga abinda ya gabata daga farkon Sura zuwa nan kuma wannan shi ne abu mai TasiriFadinsa:Ga duk wanda yake da Zuciya (ta hankalta).To wannan shi ne Mahallin da zai karba, kuma abin nufi da shi shi ne Zuciya Rayayyiya wacce take fahimtar sakon AllahKamar yadda Allah Madaukakin Sarki ya ce:Lallai cikin wann nan ba komai ba ne face wa'azi sa kuma Qur'ani mai bayani domin a wa'azantar da RayayyeAi mai rayayyiyar zuciyaSannan fadinsako wanda aka jefa masa jiAi wanda ya bada jinsa kuma yai saurara da jinsa zuwa abinda ake fada a gare shi, kuma wannan sharadin yana tasiri wajen maganaSannan fadinsakuma yana mai halarto da ZuciyarsaAi yana mai harto da a Zuciyarsa baya kautar da itaIbn Kutaibah ya ce:Ka saurari Littafin Allah kuma yana mai halarto da Zuciyarsa da fahimta baya rafkana ko mantuwakuma wan nan yana nuni zuwa abin da yake hana tasirantuwa, kuma shi ne rafkanar zuciya da buyanta ga barin fahimtar abinda ake fada mata da kuma Nazari a cikinsa da yin kyakkayawan Duba to idan aka samu maisa tasirin shi ne Al'qur'ani kuma aka samu wurin karba shi ne zuciya rayayyiya, kuma aka samu sharadin shi ne saurararawa, kuma aka kore Mai hanawa shi ne shagaltuwar zuciya da kuma sakwarkwacewar ta daga Ma'anar Kira, da kuma kaucewarsa daga kan turba zuwa wani abu daban, sai tasirin ya faru shi ne anfanuwa da kuma wa'azantuwa.

Ina rokon Allah da ya amfanar da wannan littafin kuma ya sanya shi mai albarka kuma ya datar da Marubucinsa ga dukkan Alkairi

Tsira da Aminci ga Annabinmu Muhammad

Wanda ya rubuta shi: Abdullahi Bn Abdurrahaman Al'sa'ad

17/3/1428 Bayan Hijira

 Gabatarwa Babban Malami Masanin Hadisi Dr. Mahir Bn Yaseen Al'fahl Allah ya tsare shi

Da sunan Allah Mai Rahama Mai jin kai

Dukkan Godiya ta tabbata ga Allah Ubangijin Talikai kuma tsira da Aminci su tabbat ga Shugabanmu Annabi Muhammad da Alayansa da Sahabbansa baki Daya

Bayan haka

To lallai wajibin kira zuwa ga Allah yana daga cikin Mafi Cancantar Wajibai, kuma mafi wajabcin Biyayya ga AllahKuma Allah Madaukakin Sarki ya ce: "Babu wata Magana mafi kyau kamar wanda yayi kira zuwa ga Allah kuma yayi aiki nagari kuma ya ce yana cikin Musulmi.Surat Fussilat 33To ya wajaba akan kowane Musulmi cewa ya tsaya da wannan Wajibin na Addini ga Al'ummarsaAllah Madaukakin Sarki ya ce:Kace wannan shi ne tafarki na na kira zuwa ga Addinin Allah kan Basira ni da duk wanda ya biniSurat Yusuf:108kuma yana daga cinikin mafi girman Wajibai wajen isar da Addinin Allah Kwadaitarwa kan kare wahayi guda biyu Alqur'ani da Hadisi su ne Ginshikan Addini da kuma Mabubbugar Tafarki Madaidaici, kuma ruko da su shi yake samar da jin dadin Duniya da Lahira.Kuma Alqurani Maigirma shi ne mai rarrabewa tsakanin gaskiya da karya, da kuma tsakanin Haram da Halal da kuma tsakanin Rabauta da kuma Tabewa.Kuma Alqurani Maigirma yana Alkairai masu yawa da tarin Ilimai, domin koawane Alkairi da kuma Ilimi an samo shi ne daga cikin littafin Allah kuma shi ne Mai yalwar Ma'anoni da kuma girma.kuma shi ne wa'azin da Mutum zai wa'azantu da shi na Al'amuran Ubangiji da Akidar Musulunci ingantacciya, da kuma kyawawan halaye masu girma,kyawawa, da kuma kyawawan Ayyuka.kuma shi ne Wa'azi mai girma wanda ya ke mai shiga jiki, da kuma labari masu girma da kuma Zancen Ubangiji, kuma babu abinda yake gyara zuciya sai Zancen Ubangiji.

Sannan kuma cewa yana daga cikin abinda yake Jawo farin cikin Rayuwata in gabatar da wannan littafin mai daraja Hadisai Arba'in game da Alquran.ga Dan uwanmu Shiekh Ahmad Abdurrazak Al-Ibrahim Al-angary Allah ya datar da shi da dukkan Alkairi,

Kuma littafi ne duk da kanakantar girmansa da kuma takaitattun Kalmominsa littafi ne mai Girma kuma mai Amfani, kuma mai amfani ga kuma suna bukatar kwatankwacinsa wajen dawowa zuwa ga littafin Allah a wani irin zamani wanda fitintinu suka sauka ga Mutane wanda Allah ne kadai ya sansu

kuma an Buga wannan littafi sama da Bugawa kuma an fassara shi kuma wanda ya wallafa shi ya kyautata wajen tara shi da kuma Rairarye Hadisan sa

Kuma ina rokon Allah ya rubuta masa dacewa da kuma gamdakatar, don ya gabatarwa makaranta babbar Hidima da sake buga wannan littafi, kuma Dan uwa Marubucin yana da matukar sha'awa wajen hidimtawa Hadisan Annabi wajen koya da koyarwa da kuma Rairayewa.

Kuma a Karshe ina gabatar da godiyata Mai yawa ga Mai bincike akan ya zabo wannan littafi, da kuma gabatar da shi don hidimta masa da kuma kulawa da shi, kuma ina rokon Allah gareni da shi haka baki dayan Musulmi da kyakkyawan dacewa a cikin Hidimar wannan Addini ta hanyar yada Ilimin Shari'ah

Wanda ya rubuta shi

Dr. Mahir Yaseen Al'fahl

Malamin Hadisi da kuma Fiqhun Mazhabobi

a Kwalejin Iliman Musulunci - Jami'ar Anbar

10\6\1432 Daga Hijirar Annabi tsira da Amincin Allah su tabbata ga Allah

 Wanda ya Rubuta: Dr. Hamad Al-Tamimi: Hadisai Arba'in game da Al'qura'ni

Wannan littafi ya futo ne "Hadisai Arba'in game da Al'qurani"kuma an bugashi da daukar nauyin Shiekh Abdullateef Bn Sulaiman Bn Abdullateef Al-Ibrahim Al-angari, kuma littafi ne babu irinsa a lokacinsa, kuma wanda ya wuce wadanda suka gabace shi

Wannan littafin yayi fuce a sunansa haka abinda ya kunsa, kuma Manyan Malaman Hadisi sunyi masa Shaida da cewa bashi da tsara kafinsa, bugu da kari ga ingancin Hadisan sa wadan da aka kawo a cikin sa da abin da ya kunsa, kuma Hakika Mawallafin wannan littafin yabi tsarin Bukari, kuma hakika ya sanya Babunan Unwaninsa ya tsamo su ne daga Hadisan da suka zo a cikinsa kuma an gabatar da shi ga gungun Malamai kuma wadanda suka gabatar da littafin Manyan Malaman Hadisi guda biyu Abdullahi Bn Abdurrahman Al-Sa'ad da kuma Saleh Bn Sa'ad Al-luhaidan,da Wasun su kuma sun yabe shi da kyakkayawan yabo, kuma mafi kyawunsa.

kuma hakika duk wanda ya sami kwafin wannan littafin to yayi bayaninsa sabida abinda yake cikinsa na fa'idoji masu yawa ga Daliban Ilimi cikin abin da yake da Dangantaka da littafin Allah Madaukakin sarki

Kuma Allah ya datar da Mawallafin littafin, kuma wanda ya buga liittafin, da wanda ya raba shi, da wanda yayi masa sharhi ya yadashi a tsakanin Daliban Ilimi ga dukkan abin da ya yake so kuma ya yarda da shi, lallai cewa shi ne Majibinta hakan kuma mai iko akan hakan.

Kuma wanda ya rubuta wannan shi ne Masoyin daliban Ilimi kuma mai jin tausayinsu

Wanda ya rubuta: Dr. Hamad Al-tamimi Hadisai Arba'in game da Al'qurani

- 9/5/2010 A ranar :- 25/5/1431

Madogara: Shafin yanar Gizo Al'alouka

 Gabatarwar Mawallafi

Da sunan Allah Mai Rahama Mai jin kai

Dukkan godiya ta tabbata ga Allah Ubangijin Talikai, Kuma tsira da Aminci su tabbata ga Shugabanmu Annabi Muhammad da Alayansa da Sahabbansa baki daya.

Bayan haka

Wannan shi ne Nassin: Hadisai Arba'in game da Al'qurani, wanda ya kunshi Hadisai Arba'in wadanda suka inganta daga Annabi kan Falalar Alqur'ani da Hukunce Hukuncensa da kuma Ladabansa

Kuma nayi kokarin cewa zan sanya Hadisi mai makusanciyar Ma'ana kuma wanda yake Maisaukin bayani don yai saukin haddace shi kuma a amfana da shi da kuma aiki da shi

Kuma duk wanda lura da Hadisai wadan da suka zo cikin magana kan Alqur'ani da Falalolinsa, kuma cewa zai samu ba wai kawai sun kebanta bane da haddar Alqur'ani kawai.

Da kulawa da Harafansa da Tajwidinsa da kuma rerashi, cewa ma duk wanda yake karanta Hadisai kuma ya lura da su zai samu cewa sun zo ne da kwadaitarwarwa kan Ilimi da kuma aiki da shi, da kuma Hadda.

Kuma a karshe ina kiran Yan uwana Maza da Mata zuwa ruko da Alqur'ani da kuma Ingantacciyar Sunnah da kuma aiki da su a fili da boye da kuma barin duk abinda ya Saba musu na Bidi'a ko Sabo ko takaitawa.

Kamar yadda na nuna a wanna littafin Hakika an rarraba shi zuwa Fasalai Kamar haka:

Fasali na farko

Hadisan da suka zo kan falalar karatun Alqur'ani da koyar da shi

Fasali na Biyu

Hadisan da suka zo kan Ladabai da hukunce Hukunce

Fasali na Uku

Hadisan da suka zo kan falalar Haddace littafin Allah da ladan Ma'abotansa

Fasali na Hudu

Hadisan da suka zo kan kwadaitarwa kan kokarin kiyaye haddar Alqur'ani da kuma Tilawarsa

Fasali na Biyar

Hadisan suka zo ciki falalar son kyautata Murya wajen karanta Qura'ni

Fasali na Shida

Hadisan da suka zo don tsarkake niyya wajen yin aiki sabida Allah maigirma da Daukaka

Fasali na na Bakwai

Hadisan da suka zo a falalar wasu surori

Wannan kuma ina rokon Allah dacewa da kuma gamdakatar da Ikhlasi cikin fada da kuma aiki

Kuma ina rokon Allah Mai tsarki don ya gafarta mana da Iyayenmu da Dangina Rayayyu da Matattu daga cikin su da Malamanmu da dukkan Musulmi Maza da kuma Mata

Allah Salati ga Annabinmu Muhammad da Alayansa da sahabbansa baki daya

Wanda ya rubutashi

Ahmad Bn Abdurrazaq Bn Muhammad Bn Zaid Al Ibrahim Al-anqary

An rubuta shi a birnin Riyadh a ranar: 25 /12/1427 bayan Hijira

Lambar Waya: 500850965/00966

E-mail:[email protected]

 Yadda ake Haddace Hadisai

 Na farko:

Manufa na haddar Hadisi shi ne Ilimi da kuma aiki da kauda Jahilci ga barin kai

 Na biyu:

Lallai cewa Hadisai sun sha banban ta wajen tsawo ko gajarta, Hakika Dan uwana mai girma cewa kai kana son tabbatacciyar Hadda a kwakwalwarka ba haddar da zata gudu bayan kwana biyu sannan ka manta ta

kuma ga wata hanya mai sauki ya kai Dan uwana

Ka dauki Hadisi daya sannan ka karanta shi sau uku, sannan ka gyara kusakuren larabcinka in akwai, sannan sai maimaita shi sau goma da sauri kadan

Ka kuma maimaita Hadisin daga karantawa 10-20 kana kallo kana mai hararo Nassin, sannan ka maimaita shi 10-30 sai dai wannan a zuci

kayi kokari ka maimaita abinda ka haddace a kowane hali a tsaye ne ko a zaune da kafin bacci da kana hanyarka zuwa Masallaci tabbas zaka samu romon hakan in Allah ya so

kayi kokari ka kiyaye waje maimaita abinda ka haddace sau dari kuma ko yaushe adadin karantawa ya karu to haddar zata dada tabbata

kuma daga cikin ya wajaba bayaninsa cewa Mutane sun sha banban wajen hadda kuma kowanne hali ka sami kanka zaka samu lada kan hakan in Allah ya so

 Gabatarwar Littafin

Da sunan Allah Mai Rahama Mai jin kai

Dada Sarkin Muminai Baban Hafsu Umar Dan Khattab Allah ya yarda da shi ya ce:Naji Manzon Allah tsira da Amincin Allah su tabbata a gare shi ya ceDukkan ayyuka sai da niyya kuma kowane Mutum da irin niyyar da yayi to duk wanda yayi Hijira sabida Allah da Manzonsa to ladan sa yana ga Allah da Manzonsa, kuma duk wanda yayi Hijira domin neman Duniya ko wata mata da yake son Aura to ladan Hijirarsa yana ga abinda yayi Hijira sabida shi.Bukhari da Muslim ne suka rawaito shi

Ta'aliki:

Mawallafin ya ce: cewa na fara da wannan Hadisi ne sabida koyi da magabatanmu, da kuma koyi da Limamin masu Hadisi babu mai ja kan hakan shi ne Abu Abdullahi Albkhari a cikin Sahihinsakuma hakika magabata sun kasance na wannan Al'umma suna son bude littafi da wannan Hadisin kamar yadda Imam Abdurrahman Bn Mahdi - Allah ya yarda da shi - Duk wanda yaso wallafa wani littafi to ya fara da Hadisin Umar bn Khattab - Allah yarda da shi - Cewa kowane aiki sai da Niyya a cikin kowane BabiTo sabida haka na fara littafi na Hadisai Arba'in da suke Magana kan Alqurani, don fadakar da kaina da kuma mai karatu da kuma Dalibi kan gyara Niyya, cikin Ayyukanmu Na fili da na boye

 Fasali na farko

 Hadisan da suka zo kan falalar karatun Alqur'ani da koyar da shi

 Hadisin farko

Falalar Koyar da Alqur'ani

Daga Abu Huraira Allah ya yarda da shi ya ce:Manzon Allah tsira da Amincin Allah su tabbata a gare shi ya cekuma wasu Mutane basu hadu a wani daki daga cikin Dakunan Allah ba suna karanta littafin Allah kuma suna koyar da shi a tsakaninsu sai nutsuwa ta sauka a kansu kuma Rahama ta rufe su kuma Mala'iku sun kewaye su kuma Allah ya ambace su cikin wadanda suke gurinsa, kuma duk wanda aikinsa ya maida shi baya to dangantakarsa ba zata shi yayi gaba baMuslim ne ya Rawaito shi da Kuma Abu Daud da kuma wanin su

Ta'aliki:

Wannan Hadisi ya bai kunshi Jama'ar ba kawai ya game daidaiku ma da ace Mutum daya zai zauna shi kadai kuma ya ambaci Allah to zai sami wannan Falalar da aka ambata.

 Hadisi na Biyu

Kowane Harafi daya daga littafin Allah za'a bada ladan kyawawan ayyuka goma

Daga Ibn Mas'ud Allah ya yarda da shi ya ce:Manzon Allah tsira da Amincin Allah su tabbata a gare shi ya ceDuk wanda ya karanta littafin Allah to yana da lada kuma kowane lada za'a ninkashi goma amma bazance Alif lameem harafi daya bane, sai ince Ali harafi Meem harafi neTurmizi da Al-darimi ne suka Rawaito kuma Abu Isa ya ce wannan Mai kyau ne kuma ingantacce kuma GharibiKuma Albani ya inganta shi, kuma na tambayi Malaminmu Abdullahi Al'sa'ad game da shi ya: bashi da wani aibi.

 Hadisi na Uku:

ceton Alqurani ga Ma'abotansa Ranar alkiyama

Daga Abu Umama Allah ya yarda da shi ya ce:Naji Manzon Allah tsira da Amincin Allah su tabbata a gare shi ya ceKu karanta Alqurani domin zai zo Ranar Alkiyama mai ceton Ma'abotansaMuslim ya raaito shi

Ta'aliki:

A cikin wannan Hadisi tabbatar da ceton Alqurani a ranar Akiyama bisa sabanin ceton da masu ceton .Kuma ceto ba zai yiwu sai ga Masu Kadaita Allah amma Mai shirka bashi da wani ceto koda kuwa ya fi kowa Haddar Qur'ani Domin aikinsa an bata shi tun daga Duniya sabida Shirka kuma ba za'a taba karbar komai daga gare shi ba a lahira, Allah ya tsare mu daga Shirka da masu yinta

 Hadisi na Hudu:

Kwatankwacin Muminin da yake karanta Alqurani da Munafikai

Daga Abu Musa Al'ash'ary Allah ya yarda da shi ya ce:Manzon Allah tsira da Amincin Allah su tabbata a gare shi ya ceKwatankwacin Muminin da ya ke karanta Alqur'ani kamar lemon Zaki ne Kanshin dadi haka ma Dandanonsa, kuma kwatankwacin Muminin da baya karanta Alqur'ani kamar Dabino ne bashi da kanshi amma dandanonsa Zaki, kuma Munafikin da yake karanta Alqurani kamar Nana ne kanshinsa dadi amma dandanonta daci, kuma kwatankawacin Munafikin da baya karanta Alqura'ni kwatankwacin Guna ce batada Kanshi kuma dandanonta daci.Muslim ya Rawaito da Buhari kuma sun hadu a lafazin Fajiri a maimakon - Munafuki

Ta'aliki:

Kwatankwacin Lemon Tanjirin

Kwatankwacin Lemon Tanjirin ya hade dadin dandano da kuma dadin Kamshi kuma ana kiransa da lemon zaki

Guna

Guna: wani tsiro ne da yae yado akan Kasa kamar kankana, kuma "ya'yan sa sunyi kama da na Kankana sai dai su kanana ne tayi fuce wajen Daci

 Hadisi na Biyar

Ladan Gangaran a Qur'ani da kuma wanda yake guragura a cikinsa

Kuma daga Nana Aisha Allah ya yarda da ita ta ce:Manzon Allah tsira da Amincin Allah su tabbata a gare shi ya ceGangaran wajen Karatun Quran yana tare da Manyan Mala'iku Masu biyayya ga Allah, kuma wanda yake karatu kuma yake guragura a cikinsa yana mai shan wuya to yana da lada biyu.A kuma cikin wata RiwayarWanda yake karanta shi kuma yana yi masa wahala akansa yana da lada biyuBuhari da Muslim ne suka rawaito amma lafazin na Muslim ne da kuma Ma'abotan Litattafan Sunan

Ta'aliki:

Gwanin Alqurani

Shi ne Haziqi kuma mai iya Tajawidi wanda yake karatu ba tare da tantama ba ko kusakurai kuma bayajin wahalar karatun sabida kyawun Haddarsa da Karatun sa

Kuma yake guragura a cikin karatun sa

Shi ne wanda yake gura gura a cikin karatunsa don raunin Haddarsa to yana da lada biyu ladan Karatu da ladan wahalar karatun da wahalarsa

 Hadisi na Shida

Falalar Karatun Alqurani a cikin Sallah

Daga Abu Huraira Allah ya yarda da shi ya ce:Manzon Allah tsira da Amincin Allah su tabbata a gare shi ya ceShin dayanku yana son idan ya koma ga Iyalansa ya Taguwoyi Uku Masu ciki Manya ? sai muka ce ey sai ya ce to Ayoyi Uku da zai karanta su a cikin Sallarsa to sunfi Taguwoyin Uku Masu ciki kuma Manya.Muslim ya raaito shi

Ta'aliki:

Takuwa Mai Ciki kuma Babba kuma anai mata Jam'i da Taguwoyi

 Hadisi na Bakwai

Falalar Wadan da suke aiki da Qur'ani

Daga Nawwas Dan Sam'an Allah ya yarda da shi yana cewa:Naji Manzon Allah tsira da Amincin Allah su tabbata a gare shi ya ceZa'a zo da Qur'ani a ranar Alkiyama da kuma wadan da suke aiki da shi Suratul Baqara tana yi musu jagora da Suratu Aal Imran, kuma Annabiya buga Misali guda uku da su, kuma ban manta da su ba, ya ce: Kamar Gizagizai, suna masu masu Duhu, a tsakaninsu da wani Haskekai ka ce Tawagar tsuntaye ne sun yi Sahu, suna kare Ma'abocinsu.Wannan lafazin Ahmad ne da Muslim daga Ishak Bn Mansour ya ce: Yazid Dan Abdu Rabbih ya bamu Labari da wannan Sanadin sai dai ya canza dai dai Tana yi musu Jangora, a Maimakon tana Jayayya.Daga Abu Musa Allah ya yarda dashi daga Manzon Allah tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi ya ce:Kwatankwacin Muminin da yake karanta Alqur'ani kuma yake aiki da shi Kamar Lemon Zaki Dandanonsa Zaki da haka Kanshinsa, kuma kwatankwacin wanda baya Karanta Al'qur'ani kuma yake aiki da shi Kamar Dabino ne Ga dadin Dandano kuma bashi kan shiBuhari ne ya rawaito shi

Ta'aliki:

Ibn Al-qayyim ya ce:Ma'abotan Qur'ani su ne Masanan sa kuma masu aiki da shi koda kuwa basu haddace shi ba a kwakwalwarsu, kuma duk wanda ya haddace shi bai kuma fahimce shi ba kuma baya aiki da shi ba to baya cikin Ahalinsa kuma duk wanda ya iya Harafansa iyawa,Zaad Al'Ma'adKuma Annabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi ya ce:Kai kace Gizagizai guda biyuAi ladan Surorin Bakara da Ali Imran Kamar wadansu giza gizai Manya guda biyuKo gigizai biyu Bakake a tsakaninsu akwai HaskeSabida Bakinsu da haduwar su da wasu da suke saman wasu don yin Inuwa ga Mai karanta shi a ranar alkiyama daga zafin RanaSannan fadinsaA tsakaninsu akwai hasken RanaAi Hasken Rana da Annuri shi ne Hasken Rana don fadakarwa kan cewa su duk da kaurinsu amma basa boye Haske.ko Kamar Garke biyu ko Wata TawagaAi Garke biyu ko Wata TawagaDaga Tsuntsaye da suke SahuAi sun yi Sahu Kamar yadda Masu Sallah suke yiSuna Jayayya da kuma kariyaAi Suna Jayayya da kuma kariyaGa Ma'abocinsuWanda ya kasance ya dawwama wajen Karatun Alqur'ani kuma yana aiki da shi

 Hadisi na Takwas

Falalar Karatun Surat Albakara a cikin gida

Daga Abi huraira Allah ya yarda dashi daga Manzon Allah tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi ya ce:Kada ku Mayar da gidajenku Makabarta Cewa Shaidan yana guduwa daga gidan da ake karanta Surat Al-baqaraMuslim ya rawaito shi

 Hadisi na Tara

Falalar Mai Bayyanawa da Mai Asirta Alqur'ani

Daga Uquba Dan Amir Aljuhani Allah ya yarda da shi ya ce:Naji Manzon Allah tsira da Amincin Allah su tabbata a gare shi yana cewa:Wanda yake bayyana karatun Alqur'ani Kamar mai bayyana Sadakarsa ne kuma mai boyewa kamar Mai boye Sadakarsa neTirmithi ne ya Rawaito shi da Abu Daud da Ahmad da kuma Nasa'iAbu Isa Attirmidhi ya ce: Wannan Hadisi ne Hasan Garib kuma Albani ya Inganta shi

 Hadisi na Goma

Son Sauraron Qurani

Daga Ibn Mas'ud Allah ya yarda da shi ya ce:Manzon Allah tsira da Amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce da niKarantamun Alqur'ani Sai ya ce: Ya Manzon Allah in karanta Maka bayan kai aka saukarwa sai ya ce ni ina sha'awar inji shi daga bakin wani na sai na karanta Surat Al'nisa har nakai dai daiTo yaya idan Muka zo daga koawace Al'umma Mai mata Shaida kuma muka zo dakai mai shaida ga Wadan nan.Sai na daga kaina ko ya zungureni a gefena sai na daga kaina sai naga hawayansa suna kwaranyaMuslim da Buhari ne suka rawaito shi amma lafazin na Muslim ne

 Fasali na Biyu

 Cikin Ladabai da kuma Hukunce Hukunce

 Hadisi na sha Daya

Burin Zamatowa Wani daga cikin Ma'abotan Alqur'ani

Daga Abi huraira Allah ya yarda dashi daga Manzon Allah tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi ya ce:Babu Hassada sa a abubuwa biyu: Wani Mutum da Allah yasanar da shi Alqur'ani yana karantashi cikin dare da kuma Rana sai wani Makwabcinsa yaji shi sai yace ina ma dai nima anbani irin abinda aka bawa wane inyi irin yadda yake yi da wani Mutum da Allah ya bashi Dukiya kuma yana karar da ita a hanyar Gaskiya sai ya ce: ina ma ace ina da kwatankwacin dukiyar wane inyi irin yadda yake yiBuhari da Ahmad suka rawaito shi amma lafazin na Buhari ne

 Hadisi na Sha Biyu

Yadda Annabi yake Karanta Alqur'ani

Daga Huzaifa Allah ya yarda da shi cewa Annabi tsira da Amincin Allah su tabbata a gareshi yayi sallahya kasance idan ya wuce Ayar Azaba yana tsayawa ya nemi tsari kuma idan ya wuce Ayar Rahama sai ya tsaya kuma yayi Addu' kuma idan ya wucce tsarkake Allah sai yai TasbihiIbnu Maja ya rawaito shi kuma Albani ya inganta shiKuma daga shi dai cewa Allah ya yarda da shi nayi Sallah a gefen Annabi tsira da Amincin Allah su tabbata a gare shi wani dare sai ya karanta, ya kasance idan ya wuce Ayar Azaba yana tsayawa ya nemi tsari kuma idan ya wuce Ayar Rahama sai ya tsaya kuma yayi Addu'a.Nasa'i ya rawaito shi kuma Albani ya inganta shi

 Hadisi na sha uku

Tsawon lokacin da yake sauke Alqur'ani

Daga Abdullah Dan Umar Allah ya yarda da shi cewa Annabi ya ce da shi ka karanta Qur'ani a wata daya, sai ya ce nidai bani da karfi, sai ya ce ka karanta cikin kwana ashirin, sai ya ce bani kwarin hakan sai ya ce: to cikin kwana goma sha biyar sai yace bana jin kwarin hakan, to ka karanta cikin kwana goma, sai ya ce n bani da kwarin hakan sai ya ce ka karanta cikin kwana bakwai, kuma kada ka kara kan hakan.Buhari da Muslim suka rawaito shi da kuma Abu Daud kuma lafazin na Abu Daud ne

Ta'aliki:

wannan Hadisin daga abubuwan da Abdullahi Dan Amr Asi cewa Annabi ya shiryar da shi yayin da yaga halinsa da kuma ikonsa don haka lokacin da Abdullahi Dan Umar ya tsufa sai ya koma yana shan wahalar abinda ya saba da shi sabida yawan karatunsa da kuma aikiSai ya ce Allah ya yarda da shi Kamar inda yake a cikin BuhariIna ma dai ni na karbi saukin Annabi kuma wancananka gani na tsufa kuma nayi rauni sai ya kasance yana sauke Alqur'ani tare da Ahalinsa a kwana bakwai kuma wanda zai karanta shi da daddare sai ya karanta shi da Rana don ya samu saukin sa da daddare kuma idan yana son ya samu karfin jikinsa sai ya sha ruwa kwanaki, yana kidanyasu kuma sai ya Azumci kwatankwacinsu don tsoron kada yabar komai bayan sun rabu da Annabi yana yinsa.

Na bayyana wannan Al-amari a nan kada wani ya zaci cewa wanda ya sauke Qur'ani daga cikin Sahabbai a kwana daya ko kwana biyu wannan ya sabawa abin da Annabi yayi Umarni da shi Abdullahi Bn Amr, Ba haka abin ya ke ba kuma Jawabin hakan shi ne cewa Annabi ya Amsawa mai tambaya dai dai da halinsa da mai neman neman fatawa na Musamman Kuma tsamo Hukunce Hukunce da kuma Dalilai na baki daya, sai Hadisin cikinsa akwai Kebancewa da gamewa.

 Hadisi na Sha Hudu

Anso idan Mutum ya wuce Ayar Sujada yayi Sujadar

Daga Abu Huraira Allah ya yarda da shi ya ce:Manzon Allah tsira da Amincin Allah su tabbata a gare shi ya ceIdan Dan Adam ya karantaMuslim ne ya rawaito shiA cikin Al'sunna na AlbagawiSai ya ce kaito na an Umarci wannan da yayi Sujada ...

Ta'aliki:

Sujada ba wai tana hade da Surar sujada bane kawai, aa tana hade da baki dayan Sajadodin wadanda suke cikin Qurani wadanda suke sujada goma sha biyar

 Hadisi na sha biyar

Sabida kin daga da Qurani idan za'a cutar da wadanda suke gefe

Daga Al'bayadi Allah ya yarda da shi cewa Annabi tsira da Amincin Allah su tabbata a gare shi ya futo ga Mutane suna Sallah suna daga Muryarsu da Karatu sai ya ce:Lallai mai Sallah yana ganawa da ubangijinsa to yasan da wa yake ganawa kuma kada dayanku ya daga Murya kan daya wajen karanta Qur'aniAhmad da Malik da Nasa'i daBaihaki suka rawaito shi kuma Alhaithami ya Inganta shi

 Hadisi na sha shida

Halayen Annabi tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi

Daga KatadaYa Uwar Muminai ki bamu labarin Halayen Annabi tsira da Amincin Allah su tabbata a gare shiTa ce: Ba kana karanta Qur'ani ba ? sai nace ina karantawa sai ta ce: to Halayen Annabin Allah sun kasance irin Halayen Qur'ani neMuslim ya raaito shiDaga Sa;ad Bn Hisham Bn Amir ya ce:Naje wajen Aisha Allah ya yarda da ita sai na ce:Ya Uwar Muninai ki bamu labarin Halayen Annabi tsira da Amincin Allah su tabbata a gare shiTa ce:Halayansa sun kasance Alqurani ne, baka karanta fadin Allah Mai girma da daukaka ba ne?Kuma, lalle haƙiƙa kana a kan hãlãyen kirki, manya.Surat Alqalam Aya ta 4Ahmad ya rawaito shi kuma Hadisi ne ingantacce

Ta'aliki:

Ibn Kathir ya ce:Abin da ake nufi da wannan cewa Annabi Amincin Allah a gare shi ya zamanto yana aiki da umarni da hanin qur'ani hakan ma ya zamar masa Dabi'a da halitta har takai ya bar Dabi'unsa na Asali ko yaushe aka hana shi wani abu sai ya hanu ga kuma kyawawan Dabiu da Allah ya gina shi akansu Masu girma na kunya da Karamci da kuma sadaukantaka da Kauda kai da dukkan kyawawan Halaye kamar yadda ya Tabbata.Tafsirin Surat Alqalam

 Hadisi na Sha Bakwai

Halarcin karanta Alqurani akan Dabba da kuma halarcin Maimaita Aya a cikin sa

Daga Abdullahi bn Mugaffal Al'muzni Allah ya yarda da shi ya ce:Naga Manzon Allah a Ranar Bude garin Makkah yana kan Taguwarsa yana karanta Surat Al'fath kuma yana Maimaita AyoyinBuhari da Muslim suka rawaito shi da kuma Abu Daud kuma lafazin na Abu Daud ne

Ta'aliki:

Tarji'a

o, yãyã, idan Mun zo da shaidu daga dukkan al'umma, kuma Muka zo da kai a kan waɗannan, kana mai shaida!o, yãyã, idan Mun zo da shaidu daga dukkan al'umma, kuma Muka zo da kai a kan waɗannan, kana mai shaida!Maimaita Karatu: irinsa ne dai Maimaita kiran Sallah

 Hadisi na ShaTakwas

Hanin tafiya da Qur'ani zuwa garin Kafirai da Abokan gaba idan aka ji tsoron tozarta shi a Hannunsu

Daga Abdullahi Dan Umar ya ce:Annabi ya hana tafiya da Qur'ani zuwa garin Abokan GabaBuhari Da Muslim suka rawaito shiA wata riwayar kuma ta Muslim daga Nafi'u daga Dan Umar ya ce:Manzon Allah tsira da Amincin Allah su tabbata a gare shi ya ceKada kayi tafiya da Qurani don ni bana amince maka Abokan gaba ba zasu tozarta shi ba

Ta'aliki:

Malamai sun ce:

Idan aka aminta cewa Qurani ba za'a yaga shi ba ko a jefar da shi a kasa ko Kafiri ya taba shi to halarta ayi tafiya da shi

 Hadisi na sha tara

yaya zai yi wanda ya rkirkice a karanta Qur'ani sabida tsananin Gyangyadi

Da hadisin Abi huraira Allah ya yarda dashi daga Manzon Allah tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi ya ce:Idan Dayanku o, yãyã, idan Mun zo da shaidu daga dukkan al'umma, kuma Muka zo da kai a kan waɗannan, kana mai shaida!Muslim da Ahmad da Abu Daud da Ibn Majah da Nasa'i ne suka Rawaito da wasun su ma

Ta'aliki:

FadinsaSai yake ta bata Al'quraniAi ya kasa ci gaba kuma harshensa ya rike sabida yawan Gyangyadi sabida haka sai ya bar karatun

 Hadisi Na ashirin

Fadin Mai koyar da karatu ga Mai Mai karatu Ya isa haka

Daga Ibn Mas'ud Allah ya yarda da shi ya ce:Manzon Allah tsira da Amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce da ni:Karanta mun sai na ce: o, yãyã, idan Mun zo da shaidu daga dukkan al'umma, kuma Muka zo da kai a kan waɗannan, kana mai shaida!To, yãyã, idan Mun zo da shaidu daga dukkan al'umma, kuma Muka zo da kai a kan waɗannan, kana mai shaida!Ya ce Ya Isheka yanzu sai ya waiwaya zuwa gare shi sai ya ga idanunsa suna zubar da hawayeBuhari ne ya rawaito sho

 Fasali na Uku

 Hadisan da suka zo kan falalar Haddace littafin Allah da ladan Ma'abotansa

 Hadisi na Ashirin da Daya

Cewa duk wanda ya koyi Al'qurani kuma ya koyar da shi ya kasance mafificin a cikin wannan Al'umma kuma mafi Alkairin ta

Daga Abu Abdurrahman Al'sulami daga Usman Dan Affan -Allah ya yarda da shi daga Annabi ya ce:Mafi Alkairinku wanda ya koyi Al'qu'ani kuma ya koyar da shiBuhari ne ya rawaito shoA wata riwayar kuma ta Buhari da Tirmizi daga Usman bn Affan -Allah ya yarda da shi- ya ce:Annabi Amincin Allah a gareshi ya ce:Cewa Mafifitanku shi ne wanda yasan Al'qur'ani kuma ya koyar da shiAbu Abdurrahman Al'sulamiWancan shi ne ya zaunar da ni a Mazauni na wannan

 Hadisi na Ashirin da Biyu

Daukakar Ma'abota Al'qurani koda kuwa su bayi ne

Daga Nafi'a Bn Abdulharith cewa shi ya gamu da Umar bn khattab a Usfan kuma ya kasance ya sa shi aiki a Makka sai ya ce da Umar wa kabarwa Mutanen kwari (Alwad) ? sai ya ce :wani Mutumi daga cikin Barorinmu ? sai Umar ya ce da shi Kadora musu Baro ? sai ya ce: Lallai cewa shi ai Makarancin Al'Qura'ni ne kuma yasan raboan Gado, kuma Alkali ne: sai Umar ya ce: Amma cewa Annabinku ya ce:Lallai cewa Allah yana daga Darajar wasu Mutane da wannan littafin kuma ya sauke Darajar wasuMuslim da Ahmad suka rawaito shi amma lafazin na Ahmad ne

Ta'aliki:

FadinsaLallai cewa shi Makarancin Alqur'ani ne kuma masanin Rabon gado kuma AlkaliCikin sa akwai nuni zuwa ga abinda ya gabata basu kasance Makaranta ba kawai sun kasance Masanan Addini ne kuma cikin kowane Fanni daga Fannoni kuma haka ne ya kamata ga Mahaddaci Qur'ani yayi ilimin Addini n Allah kada ya takaita kan Ilimin Kira'o'i kawai kuma duk wanda ya karanta Tarihin Makaranta Magabata zai samu cewa su futattu ne cikin kowane Fanni na Shari'ah.

 Hadisi na Ashirin da uku

Ma'abotan Alqurnai Suna Mutanen Allah kuma kebantattunsa

Daga Anas Allah ya yarda da shi ya ce:Manzon Allah tsira da Amincin Allah su tabbata a gare shi ya ceLallai Allah yana da Mutanensa daga cikin Mutane sai ya ce su waye ya Manzon Allah ? sai ya ce Ma'abotan Alqura'ani suna Mutanen Allah kuma kebantattunsaNasa'i da Ahmad suka rawaito shi kuma Albani ya inganta shi

 Hadisi na Ashirin da Hudu

Falalar Ma'abocin Alqurani idan ya shiga Aljannah

Daga Abdullahi Dan Amr Allah ya yarda da su ya ce Manzon Allah tsira da Amincin su tabbata a gare shi ya ce:Za'a ce da Ma'abocin Alqurani ka karanta ka daukaka kamar yadda kake karantawa a Duniya to cewa Matsayinka zai tsaya ne a karshen Ayar da ka karanta.Wannan Hadisin Abu Daud ya fitar da shi da wannan Lafazin kuma Ahmad ya Rawaito shi dai da Tirmithi da Nasa'i kuma Abu Isa ya ce wannan Hadisi ne Mai kyau kuma ingantacce kuma Albani ma ya Inganta shi

 Hadisi na Ashirin da biyar

Falalar Makarancin Alqurani da abinda yake samu na lada mai girma

Daga Buraida Allah ya yarda da shi ya ce: Na kasance ina zaune a wajen Annabi sai naji si yana cewa :Kuma cewa lallai Ma'abocin al-Qur'ani zai zo Ranar alkiyama , lokacin da za'a tsago kabarinsa kamar mutum wanda ya sha wuya, sai ya ce da shi kasan ni? sai ya ce: ban sanka sai ya ce: Nine Abokin Al-Qur'ani wanda na saka ka kishirwa a lokacin zafin rana, na hana ka bacci da Daddare, kuma kowane dan kasuwa yana bayan kasuwancinsa, kuma kai ne yau kana bayan kasuwancinka, sai a bashi Mulki a Hannunsa na dama kuma Dawwama a Hannun Hagu, kuma za'a sanya Masa Kambun Nutsuwa akan sa, kuma a sanyawa Iyayansa Kaya guda biyu, wanda du Duniya babu irinsu a Duniya sai su ce dame aka yi mana Tufafi irin wannan ? sai ace da su sabida Karatun qura'ni da Danku yayi sannan ace da su: ku karanta kuma ku hau Matattakalae Aljannah da dakunanta, zai kuma ta hawa matukar dai yana karatun .Wannan Hadisin Ahmad da Ubaid Bn Salam suka Rawaito shi cikin Falalar AlQur'ani da Riwayoyinsu Sikoki ne Al'muhajir Alkufi anyi Sabani wajen tabbacinsa (a Ilimin Hadisi) kuma Ibn Majah ya Rawaito shi da ibn Abu Shaiba da wasun su kuma Alhaithami ya inganta shi da Ibnu Kathir a cikin Tafsirinsa da Suyudi da kuma Albani a cikin silsila Igantacciya.

Ta'aliki:

Ma'abotan ilimi sun ce a cikin Ma'anar Kamar Mutumin da Launin sa ya canza, haka jikinsa sabida faruwar wani abu na rashin lafiya ko tafiya da waninsu, Kamar yazo a wannan sifar don ya zama yayi kama da abokinsa a Duniya, ko don ya nuna Masa cewa launin sa ya canza ne sabida launin da ya kasance a Duniya sabi da kwana karatun Qur'ani to haka Qur'ani yake a Ranar Alikyama, har ma'abocinsa yakai biyan bukatarsa a Lahira, da kuma Daukaka Madaukakiya.

 Hadisi na Ashirin da shida

Girmama Ma'abotan Al'qura'n da Daukakasu da kimantasu da nisantar cutar da su

Daga Abu Musa Al'ash'ary Allah ya yarda da shi ya ce:Manzon Allah tsira da Amincin Allah su tabbata a gare shi ya ceLallai yana daga cikin Girmama Allah girmama Ma'abocin furfura a Musulunci da Mahaddacin Alqur'ani wanda baya shige gona da iri a cikinsa ko mai sakaci da shi da kuma girmama mai Mulki mai AdalciAbu Daud da Baihaqi suka Rawaito shi kuma Albani ya Inganta shi

Ta'aliki:

FadinsaMai AdalciAi Mai Adalci a tsakanin Talakawansa

 Fasali na Hudu

 Hadisan da suka zo kan kwadaitarwa kan kokarin kiyaye haddar Alqur'ani da kuma Tilawarsa

 Hadisi na Ashirin da Bakwai

Nanata Alqur'ani da Kuma Tilawarsa

Da hadisin Abu Musa Allah ya yarda dashi daga Manzon Allah tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi ya ce:Ku rika Tilawar Alqurani Na Rantse da wanda raina yake a Hannunsa yafi saurin guduwa sama da Rakumi a cikin Dabaibayinsa.Buhari Da Muslim suka rawaito shiDaga Nafi'u daga Dan Umar Allah ya yarda dashi daga Manzon Allah tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi ya ce:Cewa kwatankwacin Ma'abocin Alqurani Kamar Ma'abocin Dabaibayayyun Rakuma ne idan ka lazance ta sai ta Zauna idan kuma ka yi watsi da ita sai ta tafiBukhari da Muslim ne suka rawaito shi

Ku rika Tilawar Alqurani Na Rantse da wanda raina yake a Hannunsa yafi saurin guduwa sama da Rakumi a cikin Dabaibayinsa.

Buhari Da Muslim suka rawaito shi

Daga Nafi'u daga Dan Umar Allah ya yarda dashi daga Manzon Allah tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi ya ce:

Cewa kwatankwacin Ma'abocin Alqurani Kamar Ma'abocin Dabaibayayyun Rakuma ne idan ka lazance ta sai ta Zauna idan kuma ka yi watsi da ita sai ta tafi

Bukhari da Muslim ne suka rawaito shi

 Hadisi na Ashirin daTakwas

Ka rika bitar Alqur'ani dare da rana in ba haka za'a Mantar da ku

Daga Musa Bin Ukuba daga Nafi'u daga Bn Umar Allah yarda da su ya ce:Manzon Allah tsira da Amincin Allah su tabbata a gare shi ya ceKuma idan Ma'abocin Alqurani ya karanta Alqur'ani dare da Rana sai ya rike shi amma in yaki hakan sai ya Manta shi.Muslim ne ya rawaito shi

Manzon Allah tsira da Amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce

Kuma idan Ma'abocin Alqurani ya karanta Alqur'ani dare da Rana sai ya rike shi amma in yaki hakan sai ya Manta shi.

Muslim ne ya rawaito shi

Ta'aliki:

Lallai Hadisan da suka zo game da Narko Mai tsanani ga wanda ya haddace Qurani kuma ya Manta shi cewa shi zai gamu da Allah yana kuturce ko wanin haka, basu inganta ba.Kawai dai babu rashin Rabo kamar na wanda Allah ya bashi shi kuma yayi masa baiwa da Haddar littafinsa kuma yana jin dadin karanta shi kuma ya haskaka masa Fuskarsa da kuma Zuciyarsa sannan kuma ya barshi sabida Sakaci da Kiwa, sannan kuma har a kwace masa wannan Haddar sabida wannan kiwar, to wannan shi ne Wanda ba shi Rabo,Babu tsumi babu Karfi sai da taimakon Allah

Kawai dai babu rashin Rabo kamar na wanda Allah ya bashi shi kuma yayi masa baiwa da Haddar littafinsa kuma yana jin dadin karanta shi kuma ya haskaka masa Fuskarsa da kuma Zuciyarsa sannan kuma ya barshi sabida Sakaci da Kiwa, sannan kuma har a kwace masa wannan Haddar sabida wannan kiwar, to wannan shi ne Wanda ba shi Rabo,

Babu tsumi babu Karfi sai da taimakon Allah

 Hadisi na Ashirin da tara

Mai zai ce wanda ya manta wata Aya ko Sura?

Daga Ibn Mas'ud Allah ya yarda da shi ya ce:Manzon Allah tsira da Amincin Allah su tabbata a gare shi ya ceKada Dayanku ya ce Na manta Aya kaza da kaza Aa ya ce an Mantar da niwannan lafazin Nasa'i ne kuma Muslim ne ya fitar da shi a wannan LafazinKada Dayanku ya ce Na manta Aya kaza da kaza Aa ya ce an Mantar da niBuhari ne ya rawaito shi daiDaga shi dai Allah ya yarda da shi ya ce:Naji Manzon Allah tsira da Amincin Allah su tabbata a gare shi ya ceTir da Mutumin da zai ce Na manta Aya kaza da kaza Aa ya ce an Mantar da nMuslim ya rawaito shi

Manzon Allah tsira da Amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce

Kada Dayanku ya ce Na manta Aya kaza da kaza Aa ya ce an Mantar da ni

wannan lafazin Nasa'i ne kuma Muslim ne ya fitar da shi a wannan Lafazin

Kada Dayanku ya ce Na manta Aya kaza da kaza Aa ya ce an Mantar da ni

Buhari ne ya rawaito shi dai

Daga shi dai Allah ya yarda da shi ya ce:

Naji Manzon Allah tsira da Amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce

Tir da Mutumin da zai ce Na manta Aya kaza da kaza Aa ya ce an Mantar da n

Muslim ya rawaito shi

 Fasali na Biyar

 Hadisan suka zo ciki falalar son kyautata Murya wajen karanta Qura'ni

 Hadisi na Talatin

Kyautata Sauti da kayata shi wajen karanta Alqur'ani gwargwadon iko

Daga Abu Huraira Allah ya yarda dashi daga Manzon Allah tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi ya ce:Allah baiyi izini ga Annabi da wani Abu ba kamar yadda yayi izini da ya kawata Muryasa da Qur'aniBuhari da Muslim ne suka rawaito shi, lafazin na Bukhari neDaga Abu Huraira Allah ya yarda da shi ya ce:Manzon Allah tsira da Amincin Allah su tabbata a gare shi ya ceBaya tare da mu wanda baya Kawata Muryarsa da Qur'aniBuhari ne ya rawaito shoDaga Barraa Allah ya yarda da shi ya ce:Manzon Allah tsira da Amincin Allah su tabbata a gare shi ya ceKu kawata Muryarku da Qur'aniAhmad da Abu Daud da Ibnu Maja da Darimi ne suka Rawaito shi kuma Albani ya Inganta shi

Allah baiyi izini ga Annabi da wani Abu ba kamar yadda yayi izini da ya kawata Muryasa da Qur'ani

Buhari da Muslim ne suka rawaito shi, lafazin na Bukhari ne

Daga Abu Huraira Allah ya yarda da shi ya ce:

Manzon Allah tsira da Amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce

Baya tare da mu wanda baya Kawata Muryarsa da Qur'ani

Buhari ne ya rawaito sho

Daga Barraa Allah ya yarda da shi ya ce:

Manzon Allah tsira da Amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce

Ku kawata Muryarku da Qur'ani

Ahmad da Abu Daud da Ibnu Maja da Darimi ne suka Rawaito shi kuma Albani ya Inganta shi

Ta'aliki:

Baya tare da mu

Ai baya kan shiriyar mu

 Hadisi na Talatin Daya

Yabon Mutum idan ya cancanci hakan kuma an Aminta da Fitinarsa

Daga Abu Musa Al'ash'ary Allah ya yarda da shi ya ce:Cewa Annabi ya ce da shiDa ka ganni ina sauraron Karatunka Jiya da Daddare hakika an baka zazzakar Murya irin ta Iyalan Annabi DaudBukhari da Muslim ne suka rawaito shia wata riwayar ta Ibn Hibban da waninsaAbu Musa ya ce : sai na ce ya Manzon Allah da na san kana nan da na Kyautata maka (Karatuna) Kyautatawa

Cewa Annabi ya ce da shi

Da ka ganni ina sauraron Karatunka Jiya da Daddare hakika an baka zazzakar Murya irin ta Iyalan Annabi Daud

Bukhari da Muslim ne suka rawaito shi

a wata riwayar ta Ibn Hibban da waninsa

Abu Musa ya ce : sai na ce ya Manzon Allah da na san kana nan da na Kyautata maka (Karatuna) Kyautatawa

Kuma hakika Malaminmu Masanin Hadisi: Abdullahi Al'sa'ad daga riwayar Ibnu hibban sai ya ce babu laifi da ita

Ta'aliki:

Dabari ya rawaito daga Umar Dan Khattab cewa ya kasance yana cewa ga Abu Musa Al'ash'ari

Ka tunasar da mu Ubangijinmu sai abu Musa ya ya Karanta kuma ya rera Murya kuma ya ce: wanda duk yake da ikon rera murya da Alqur'ani irin rerawar Abu Musa to yayi

Kuma haka an rawaito daga Ibn Hibban da wani lafazin

 Fasali na Shida

 Hadisan da suka zo don tsarkake niyya wajen yin aiki sabida Allah maigirma da Daukaka

 Hadisi na Talatin da Biyu:

Wanda yake Riya da Karatunsa

Daga Abu Huraira Allah ya yarda da shi a Hadisi mai tsawo ya ce:Naji Manzon Allah tsira da Amincin Allah su tabbata a gare shi ya ceCewa Lallai farkon wanda za'a fara yiwa Hisabi a Ranar Al'qiyamasai fadi Wani Mutum da Yakoyi Ilimi kuma ya koyar da shi kuma ya Karanta Al'Qura'ni sai a zo sahi kuma a nuna masa Ni'amominsa sai ya Shaida su yace to yaya kayi da su? sai ya ce: Na koyi ilimi kuma na koyar da shi kuma na Karanta Al'Qur'ani sabida kai, sai ya ce: Karya kake kaidai koyi Ilimi don ace kai Malami ne kuma ka karanta Al'Qurani don ace kai Makaranci ne to an fada sannan sai ayi Umarni da a jashi akan fuskarsa har sai an jefa shi wutaiMuslim ne ya rawaito shi da waninsa kuma wannan yankin Hadisin

Naji Manzon Allah tsira da Amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce

Cewa Lallai farkon wanda za'a fara yiwa Hisabi a Ranar Al'qiyamasai fadi Wani Mutum da Yakoyi Ilimi kuma ya koyar da shi kuma ya Karanta Al'Qura'ni sai a zo sahi kuma a nuna masa Ni'amominsa sai ya Shaida su yace to yaya kayi da su? sai ya ce: Na koyi ilimi kuma na koyar da shi kuma na Karanta Al'Qur'ani sabida kai, sai ya ce: Karya kake kaidai koyi Ilimi don ace kai Malami ne kuma ka karanta Al'Qurani don ace kai Makaranci ne to an fada sannan sai ayi Umarni da a jashi akan fuskarsa har sai an jefa shi wutai

Muslim ne ya rawaito shi da waninsa kuma wannan yankin Hadisin

Ta'aliki:

Kuma cikin Wannan Hadisin yana kwadaitar kan Ikhlasin aiki sabida Allah shi kadai maigirma da daukaka.Kuma hakika naga wasu sun bar haddar wasu sun bar Haddar bayan karanta shi ko jin wannan Hadisin Sabida Narkon da ya zo a cikinsa to ya Wajaba kada wannan Hadisin ya hanashi Hadda ya wajaba yaci gaba da dagewa don Bawa yana inganta Niyyarsa ne da abinda zai iya kuma muna rokon Allah ya gyara Masa niyyarsa Allah baya tozarta duk wanda ya roke shi kuma wannan shi ne fatan mu a wajen Allah Maigirma da Daukaka.

Kuma hakika naga wasu sun bar haddar wasu sun bar Haddar bayan karanta shi ko jin wannan Hadisin Sabida Narkon da ya zo a cikinsa to ya Wajaba kada wannan Hadisin ya hanashi Hadda ya wajaba yaci gaba da dagewa don Bawa yana inganta Niyyarsa ne da abinda zai iya kuma muna rokon Allah ya gyara Masa niyyarsa Allah baya tozarta duk wanda ya roke shi kuma wannan shi ne fatan mu a wajen Allah Maigirma da Daukaka.

 Hadisi na talatin da uku

Al'qur'an Hujja ne gareka ko akanka

Daga Abu Musa Al'ash'ary Allah ya yarda da shi ya ce:Manzon Allah tsira da Amincin Allah su tabbata a gare shi ya ceKuma Al'qur'an Hujja ne gareka ko akanka Kuma dukkan Mutane suna wayar gari to ya saida kansa ko ya yanta ta ko ya hallaka taMuslim ne ya rawaito shi

Manzon Allah tsira da Amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce

Kuma Al'qur'an Hujja ne gareka ko akanka Kuma dukkan Mutane suna wayar gari to ya saida kansa ko ya yanta ta ko ya hallaka ta

Muslim ne ya rawaito shi

 Fasali na na Bakwai

 Hadisan da suka zo cikin Falalar wasu Surori

 Hadsi na Talatin da Bakwai

Falalar Suratul Fatiha

Daga Abu Sa'id Bn Al'mu'alli Almu'ally Allah ya yarda da shi ya ce: ina Sallah sai Annabi ya kirawo ni sai ban Amsa Masa ba sai na ce: ya manzon Allah ni na kasance ina Sallah ya ce: Allah ba yana cewa ba:Ku amsawa Allah da Manzon idan suka kirakuSannan ya ce bana sanar da kai mafi girman sura a cikin Alqurani kafin futa daga Masallaci ba sai ya rike Hannuna yayin da muka zo futa sai na ce: Ya Manzon Allah Kafa ce : zaka sanar dani wata sura mafi girma a cikin AlQur'ani sai ya ce:Godiya ta tabbata ga Allah, Ubangijin halittu;Su ne Bakwai cikin biyu da kuma Alqurani Mai girma wanda aka baniBuhari ne ya rawaito sho

Ku amsawa Allah da Manzon idan suka kiraku

Sannan ya ce bana sanar da kai mafi girman sura a cikin Alqurani kafin futa daga Masallaci ba sai ya rike Hannuna yayin da muka zo futa sai na ce: Ya Manzon Allah Kafa ce : zaka sanar dani wata sura mafi girma a cikin AlQur'ani sai ya ce:

Godiya ta tabbata ga Allah, Ubangijin halittu;

Su ne Bakwai cikin biyu da kuma Alqurani Mai girma wanda aka bani

Buhari ne ya rawaito sho

Ta'aliki:

Fatiha rukuni ce daga cikin Rukunan Sallah Kamar yadda ya tabbata daga Annabi kuma Sallah bata inganta sai da ita to ya Wajaba kan Musulmi to ya wajaba akan Musulmi ya gyara Karatun fatiharsa a gurin Malami wanda ya iya Qur'ani ko Mai iya Tajwidi ba tare gwalagwaso baKuma babu wani abinda zai hana ka yakai Dan uwana ka zauna cikin koyo da kuma gyara Karatunka na Fatiha tsawon Sati ko wata.Malam Uthaimin ya ce: Idan bai samu wanda zai koya masa Fatiha ba sai ya biya kudi to ya biya shin dai dai yake da wanda bai samu Ruwan Alwala ba sai ya biya kudi saya.Alikhtiyarat Ala Almumti'a

Kuma babu wani abinda zai hana ka yakai Dan uwana ka zauna cikin koyo da kuma gyara Karatunka na Fatiha tsawon Sati ko wata.

Malam Uthaimin ya ce: Idan bai samu wanda zai koya masa Fatiha ba sai ya biya kudi to ya biya shin dai dai yake da wanda bai samu Ruwan Alwala ba sai ya biya kudi saya.

Alikhtiyarat Ala Almumti'a

 Hadsi na Talatin da Baiyar

Falalar Suarar Bakara da Ali Imaran

Daga Abu Umama Allah ya yarda da shi ya ce:Naji Manzon Allah tsira da Amincin Allah su tabbata a gare shi ya ceKu karanta Qur'ani domin zai zo ranar Alkiyama yana mai ceton Ma'abotansa ku karanta urori biyu Bakara da Al-Imran cewa su zasu zo a Ranar Alkiyama kamar Giza Gizai ko kamar wata Tawagar tsuntsaye sunyi Sahu suna Kare Ma'abocinsu ku karanta Surat Albakara don Haddace ta Albarka ne kuma barinta Asara ne kuma Masu tsafi ba zasu iya ta baMuslim ne ya Rawaito shi da Kuma Abu Daud da kuma waninsu

Naji Manzon Allah tsira da Amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce

Ku karanta Qur'ani domin zai zo ranar Alkiyama yana mai ceton Ma'abotansa ku karanta urori biyu Bakara da Al-Imran cewa su zasu zo a Ranar Alkiyama kamar Giza Gizai ko kamar wata Tawagar tsuntsaye sunyi Sahu suna Kare Ma'abocinsu ku karanta Surat Albakara don Haddace ta Albarka ne kuma barinta Asara ne kuma Masu tsafi ba zasu iya ta ba

Muslim ne ya Rawaito shi da Kuma Abu Daud da kuma waninsu

Ta'aliki:

Masu sihiri

 Hadisi na Talatin da Tara:

Falalar Suratul Kahfi

Da hadisin Abu Al-tarda'i Allah ya yarda dashi daga Manzon Allah tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi ya ce:Duk wanda ya haddace Ayoyi goma daga farkon Suratul Kahfi za'a kare shi daga Fitinar DujalMuslim ne ya Rawaito shi da Kuma Abu Daud da kuma waninsuA kuma cikin wata RiwayarDuk wanda ya haddace karshen Suratul KahfiA kuma cikin wata Riwayardaga Karshen AlkahfiDaga Nawwas Bn Sam'an Alkilabi Allah ya yarda da shi a cikin Hadisi Mai tsawo ya ce:Annabi ya bada labarin Dujal sannan ya ce:kuma duk wanda ya ganshi daga cikinku to ya karanta masa Farkon Surar KahfiIbnu Maja ya rawaito shi kuma Albani ya inganta shiDaga Abu Said Alkhudiri cewa Annabi tsira da Amincin Allah su tabbata a gare shi ya ceDuk wanda ya karanta surat Alkahfi a ranar Jumu'a za'a haskaka masa haske tsawon zuwa wata Jumu'aBaihaki ne ya rawaito shi da kuma Shehinmu Abdullahi Alsa'ad

Duk wanda ya haddace Ayoyi goma daga farkon Suratul Kahfi za'a kare shi daga Fitinar Dujal

Muslim ne ya Rawaito shi da Kuma Abu Daud da kuma waninsu

A kuma cikin wata Riwayar

Duk wanda ya haddace karshen Suratul Kahfi

A kuma cikin wata Riwayar

daga Karshen Alkahfi

Daga Nawwas Bn Sam'an Alkilabi Allah ya yarda da shi a cikin Hadisi Mai tsawo ya ce:

Annabi ya bada labarin Dujal sannan ya ce:

kuma duk wanda ya ganshi daga cikinku to ya karanta masa Farkon Surar Kahfi

Ibnu Maja ya rawaito shi kuma Albani ya inganta shi

Daga Abu Said Alkhudiri cewa Annabi tsira da Amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce

Duk wanda ya karanta surat Alkahfi a ranar Jumu'a za'a haskaka masa haske tsawon zuwa wata Jumu'a

Baihaki ne ya rawaito shi da kuma Shehinmu Abdullahi Alsa'ad

Ta'aliki:

Ana fara karanta Surat Alkahfi bayan kiran Sallar Asuba har zuwa kiran Sallar Magriba kuma wannan ita ce rana a shar'ance ga MusulmiKuma wasu daga cikin Ma'abotan Ilimi suna ganin kuma: Halarcin karanta surar daren Juma'a kuma lokacin dai yana da yalwa

Kuma wasu daga cikin Ma'abotan Ilimi suna ganin kuma: Halarcin karanta surar daren Juma'a kuma lokacin dai yana da yalwa

 Hadsi na Talatin da Bakwai

Falalar Suratul Mulk

Daga Abu Huraira daga Annabi tsira da Amincin Allah su tabbata a gare shi cewa ya ce:Lallai cewa wata Sura a cikin Alqurani tana da Ayoyi Talatin ta ceci wani Mutum har sai da aka gafarta masa ita ce: Surar TabarakaAhmad ya rawaito shi da kuma Ma'abotan Sunan, da kuma Tirmithi ya ce: Hadisi ne Mai kyau kuma Ingantacce haka AlbaniDaga Ibn Mas'ud Allah ya yarda da shi ya ce:Manzon Allah tsira da Amincin Allah su tabbata a gare shi ya ceSurat Tabaraka ita ce Mai hana Azabar Kabarikuma Alshajari ne ya rawaito shi a cikin Al'amali Alkhasisiyya kuma Albani ya Inganta shi a cikin Sahih Al'jami'a

Lallai cewa wata Sura a cikin Alqurani tana da Ayoyi Talatin ta ceci wani Mutum har sai da aka gafarta masa ita ce: Surar Tabaraka

Ahmad ya rawaito shi da kuma Ma'abotan Sunan, da kuma Tirmithi ya ce: Hadisi ne Mai kyau kuma Ingantacce haka Albani

Daga Ibn Mas'ud Allah ya yarda da shi ya ce:

Manzon Allah tsira da Amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce

Surat Tabaraka ita ce Mai hana Azabar Kabari

kuma Alshajari ne ya rawaito shi a cikin Al'amali Alkhasisiyya kuma Albani ya Inganta shi a cikin Sahih Al'jami'a

 Hadsi na Talatin da Takwas

Falalar Surar Kulhuwa da kuma Falaki da Nasi

Daga Abu Sa'id Alkhudri - Allah ya yarda - ya ce: Cewa lallai naji wani Mutum yana karanta:Ka ce: "Shi ne Allah Makaɗaĩci."Al-Ikhlas: 1Buhari da Ahmad suka Rawaito shi kuma a cikin saNa rantse da wanda raina yake a Hannunsa, lallai cewa ita tayi daidai da daya bisa ukun Qur'aniBuhari da Ahmad suka Rawaito shi kuma a cikin saKuma Mutumin ya kasance yana yana fadarsu duk inda ya zaunaBa tare da zinde kuma su yaruka ne biyu

Ka ce: "Shi ne Allah Makaɗaĩci."

Al-Ikhlas: 1

Buhari da Ahmad suka Rawaito shi kuma a cikin sa

Na rantse da wanda raina yake a Hannunsa, lallai cewa ita tayi daidai da daya bisa ukun Qur'ani

Buhari da Ahmad suka Rawaito shi kuma a cikin sa

Kuma Mutumin ya kasance yana yana fadarsu duk inda ya zauna

Ba tare da zinde kuma su yaruka ne biyu

 Hadisi na Talatin da Tara:

Falalar Ayatal kursiyyi

Daga Abu Huraira Allah ya yarda da shi ya ce:0Annabi ya wakiltani da gadin Zakkar Azumi, sai wani yazo mun yana kwasar Abincin sai na kama shi, kuma na ce: Sai na kai kararka wajen Annabi sai ya fadi Hadisin baki dayansa har inda ya isa inda Shaidan yake cewa a na Uku: ka rabu dani zan sanar da kai wasu kalmomi zasu yi maka Amfani sai na ce: wadan ne ne? sai ya ce: Idan ka tafi zuwa Shimfidarka ka karanta Ayatal kursiyyuAllah, bãbu wani abin bautawa fãce Shi, Rãyayye Mai tsayuwa da kõme.Albakara: 255Har yakai karshe Ayar, Kariya daga Allah ba zata taba gushewa daga gareka ba, kuma Shaidan ba zai taba kusantarka ba har safiya -sai na sake shi, sai na wayi gari sai Annabi ya gayamun:Mai ya faru da Mutuminka daren jiya?sai na ce: ya Manzon Allah ya raya cewa shi zai sanar da ni wasu kalmomin zasu amfanar da ni, sai na bar shi ya tafi, sai ya ce: wadan ne ne? sai ya ce dani: Idan kazo kwanciya ka karanta Ayatal kursiyyi daga farkonta har zuwa karshen AyaAllah, bãbu wani abin bautawa fãce Shi, Rãyayye Mai tsayuwa da kõme.Albakara: 255Kuma ya ce da ni: Kariya daga Allah ba zata taba gushewa daga gareka ba, kuma Shaidan ba zai taba kusantarka ba har safiya - kuma sun kasance mafi kwadayin akan Alkairi- sai Annabi ya ce: amma hakika shi ya gaya maka gaskiya amma shi makaryaci ne, ka san wa kake magana da shi tun kwana uku kai Abu Huraira ? sai ya ce Aa sai yace: Shaidan neBuhari ne ya rawaito sho

0Annabi ya wakiltani da gadin Zakkar Azumi, sai wani yazo mun yana kwasar Abincin sai na kama shi, kuma na ce: Sai na kai kararka wajen Annabi sai ya fadi Hadisin baki dayansa har inda ya isa inda Shaidan yake cewa a na Uku: ka rabu dani zan sanar da kai wasu kalmomi zasu yi maka Amfani sai na ce: wadan ne ne? sai ya ce: Idan ka tafi zuwa Shimfidarka ka karanta Ayatal kursiyyu

Allah, bãbu wani abin bautawa fãce Shi, Rãyayye Mai tsayuwa da kõme.

Albakara: 255

Har yakai karshe Ayar, Kariya daga Allah ba zata taba gushewa daga gareka ba, kuma Shaidan ba zai taba kusantarka ba har safiya -sai na sake shi, sai na wayi gari sai Annabi ya gayamun:

Mai ya faru da Mutuminka daren jiya?

sai na ce: ya Manzon Allah ya raya cewa shi zai sanar da ni wasu kalmomin zasu amfanar da ni, sai na bar shi ya tafi, sai ya ce: wadan ne ne? sai ya ce dani: Idan kazo kwanciya ka karanta Ayatal kursiyyi daga farkonta har zuwa karshen Aya

Allah, bãbu wani abin bautawa fãce Shi, Rãyayye Mai tsayuwa da kõme.

Albakara: 255

Kuma ya ce da ni: Kariya daga Allah ba zata taba gushewa daga gareka ba, kuma Shaidan ba zai taba kusantarka ba har safiya - kuma sun kasance mafi kwadayin akan Alkairi- sai Annabi ya ce: amma hakika shi ya gaya maka gaskiya amma shi makaryaci ne, ka san wa kake magana da shi tun kwana uku kai Abu Huraira ? sai ya ce Aa sai yace: Shaidan ne

Buhari ne ya rawaito sho

 Hadisi na Arba'in

Falalar Ayoyi biyu na Surat Albakara

Daga Abu Musa Al'ash'ary Allah ya yarda da shi ya ce:Manzon Allah tsira da Amincin Allah su tabbata a gare shi ya ceAyoyi biyu a karshen Suratul Bakara duk wanda ya karanta su da Daddare to sun isar masa kariyaBuhari Da Muslim suka rawaito shi

Manzon Allah tsira da Amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce

Ayoyi biyu a karshen Suratul Bakara duk wanda ya karanta su da Daddare to sun isar masa kariya

Buhari Da Muslim suka rawaito shi

Ta'aliki:

Ma'ana ya isar Masa ai zasu kiyaye shi daga Sharri kuma zasu kare shi daga abin ki.

Ya cika da godiyar Allah a Ranar 25\12\1427 Bayan Hijira

Wanda ya Rubuta Ahmad Bn Abdurrazaq Bn Muhammad Aal Ibrahim Al-Angary

Dukkan godiya ta tabbata ga Allah wanda da Ni'amarsa ne kyawawan Ayyuka suke cikaKuma tsira da Aminci ga Annabin mu Muhammad da ALayan sa da kuma Sahabban sa da Mabiyan su da kyautatawa har zuwa Ranar Alkiyama.

Kuma tsira da Aminci ga Annabin mu Muhammad da ALayan sa da kuma Sahabban sa da Mabiyan su da kyautatawa har zuwa Ranar Alkiyama.