Wannan wani littafi ne takaitacce kuma cikinsa akwai abinda ya wajaba Mutum ya sanshi kuma ya kudurce shi na abubuwan da suka shafi kadaita Allah, da kuma Tushen Addini da wasu abubuwan da suke da alaka da shi wadanda aka samo su daga litattafan Tauhidi na Manyan Malaman Mazhabobin nan guda Hudu. Iman Abu hanifa, Imam Malik, Imam Shafi'i, Imam Ahmad bn Hanbal, da kuma mabiyansu - Allah ya yi musu Rahama, kuma su ne wadanda Mutane suka hadu kan cewa Akidar su tana kan Akidar Ahlusunnah da Jama'a babu wanda kuma ya saba kan hakan.