110 - Suratu Al'nasr ()

|

(1) Idan taimakon Allah ya zo da cin nasara.

(2) Kuma ka ga mutane suna shiga addinin Allah, ƙungiya-ƙungiya.

(3) To, ka yi tasbihi game da gõde wa Ubangijinka, kuma ka nẽme Shi gafara, lalle Shi (Ubangijinka) Ya kasance Mai karɓar tũba ne.