110 - Suratu Al'nasr ()
|
(1) Idan taimakon Allah ya zo da cin nasara.
(2) Kuma ka ga mutane suna shiga addinin Allah, ƙungiya-ƙungiya.
(3) To, ka yi tasbihi game da gõde wa Ubangijinka, kuma ka nẽme Shi gafara, lalle Shi (Ubangijinka) Ya kasance Mai karɓar tũba ne.