Littafine da ya tara ingantacciyar akida da ta zama wajibi akan kowanne musulmi ya kudurceta, kamar bayanin shikashikan musulunci da kaddara da abinda ya zama wajibi a sani akan sahabbai.
Littafi ne da ya kunshi bayani akan rukunan musulunci da sharuddan Kalmar shahada da kuma tsarin karantar da al’umma, da bayani akan alwala da sallah, da kuma yadda ake shirya janaza da yi mata da tsoratarwa akan shirka, da bayanai akan kyawawan dabi’un musulunci.
Yayibayani ne akanTauhidi da kumafa’idojinsa, da hatsarindakecikinshirka da munafunci da ayyukanjahiliyya, kumayayibayaniakankongiyoyinawannanzamanikamarwadandasukemusunakwai Allah da kwaminisanci, da kumahukuncinshigaciki, hakananyayi Magana akanhakkokinAnnabi, da naiyalanshi da nasahabbanshimasudaraja, yaambacibidi’o’i da bayyanarsu da kumahatsarindakecikinta, da takaitaccanmisaliakanbidi’o’inwannanlokacin.
Mawallafin littafin ya ambaci wadansu gimshikai guda shida, kuma ya yi bayanin abinda ya shafi hakkin Allah akan bayinsa da kuma cewar shi Allah ya umarce su ne da kadaitashi, kuma ya hana su su rarraba ya umarce su da hadin kai, kuma ya maida martini ga rudanin da makiya musulunci suke kawowa.
Malan yayibayanine akan yima allah bauta da kuma yarda da kaddara da hukumcin kafirtarda mutane da qaidodinta ,dakuma bayani akan azabar kabari da lahira ,da hukumcin karantawa mamaci al qur ani ,dakuma Waliyyan allah da bam baci tsakaninsu da Waliyyan shaitan da masu sihiri da bokanci , dakuma fa lalan sahabbai da makaminsu awajan allah , dasauran abubuwa masu mahimmaci da yakkamaci musulmi yasansu acikin addininsa da aqidarsa.
Bayanin akan tauhidi da shirka da wasu nau aukan shirka da wasu kefadawa acikinsu da gar gadi akansu da wasu mas aloli masu mahimmaci akan tauhidi wanda wajibine akan kowane musulmi yasan su dan gudun fadhawa acikin shirka.
Abindake wajibi akan kowane musulmi yasansu daga cikin nau aukan ibada dakuma wasu kura kuran da wasu musulmai kefatdawa acikinsu, da fadakarwa akansu.
Malan yayi bayani akan ma anar qa idodin nan guda hudu dakuma ma himmacin fahimtar fawhidi ga kowane musulmi da musulma da hikimar halittan mutane da aljan da sharuttan karban ayukka da kuma sauransu.